Showing 387001 words to 390000 words out of 512766 words

Chapter 130 - Asanadin Makwabtaka Book 3 Hausa Novel Complete

Unknown   

27 Dec 2024

1570

ko, yanayin yadda tay Maganar da yar shagwaba, d'an murmushi taga yayi yace mata ai kawai zata taya shi zama ne ba wani abu ba, yamutsa fuska Fauzy tay yadda take ji kaman ta saki kuka don tasan ko ba wani abun dole k'ilan bai rasa ta6a wadda zai kawo d'in tunda ance yana yin hakan ita yanzu ma ta fara zargin anya bai wuce hakan, ji tayi idanun ta sun ciko da k'walla kawai sai ta sadda kanta k'asa ta daina barin kallonshi shi kuma yanata kallon ta bayan d'an wani lokaci taji ya kira sunan ta shiru ta d'an yi bata amsa ba, a duniya tana jin ba wanda ya iya kiran sunanta kaman yadda yake yi don sosae yake fitar da ko wane harafi,

"ba ki ji na kira ki ba?" Jin ya fad'i hakan yasa ta d'ago ta kalle shi idanunta sun d'an tara k'walla a hakan ma tayi kokarin maida wasu, "baki so tazo ne?" yana mata wani kallo ya tambayi hakan da sauri ta d'aga mashi kai,
"Why?"
"To ai ba kyau fa hakan kuma nasan ka sani taya wata zata zo ta taya ka zama ina laifin ko abokin ka" cikin yar karyayyar murya ta mai son yin kuka tayi Maganar, shiru yay idonshi cikin nata tana ta yan d'aure dauren fuska can taga yay wani d'an murmushi tare da ta6e baki ganin haka yasa ta maida idonta k'asa kawai sai ji tayi k'walla sun zubo mata sharr kiran sunanta ya k'ara yi ta d'ago saida yay mamakin ganin kwallan duk da bai nuna ba, ce mata yay don wata zata zo ta taya shi zama shine yasa take kuka shiru tay bata ce komai ba tana ta yan kyafcen kyafcen idanu,

"In kuma wadda zata zo d'in Wife ena ce shima hakan ba kyau ne?" kaman daga sama taji ya fad'i hakan da sauri ta tsaida idanunta kan shi ya d'age mata gira alamar ta bashi amsa, shiru tayi tana juya abunda ya fad'a a cikin ranta tunanin to wacece Matar tashi ta shiga yi can zuciyarta ta raya mata ita yake nufi ko, sai lokacin ta gane kan Maganar tun daga farko tayi zuru zuru tana kallon shi yana d'an shigar da lip d'inshi na k'asa kafin ya saki yace bata bashi amsa ba, cikin jin yar kunya tace to ai bai fad'i mata hakan yake nufi bane ita tayi tunanin wata ce kawai da ba komai tsakanin su zai kawo, d'an ta6e baki yay kafin yace yar k'arama da ita tasan kishi, Maganar dariya ta bata tasa hannunta daya sha k'unshi ta d'an rufe fuskarta kafin ta cire a d'an shagwabe tace "nifa ba yarinya bace tunda na wuce 20yrs kuma baka ga ba Secondary nike ba, kuma ai ko K'aramin yaro yana kishin abunda yake so" ita kanta ji tayi kawai ta fad'i hakan, hannu ya kai ya d'an shafi beard d'in shi murmushi ya bayyana akan fuskar shi yace mata ashe tana son shi ta d'aga mashi kai yace amman ai bata ta6a fad'i mashi ba tace to ai bata san ko bai son ta fad'i mashi hakan ba yay shiru kawai yana kallonta, tattaro k'warin gwuiwa tayi idonta a cikin nashi ta furta "I love you with all my Heart" gani tayi ya d'an fad'ad'a murmushin da yake tare da d'an ta6e baki yanayin yadda yayin sai taga kaman abunda tace bata yi mashi gwaninta ba, abunda bata sani ba shine sosae yaji dad'in Maganar duk da ba bak'uwa bace a wurin shi kullum mata cikin fad'i mashi Kalmar suke don ko yau an fad'i mashi amman tata sai yaji tayi mashi dad'i shi kanshi yana mamakin kanshi sosae yadda akai Ya fad'a son ta don sosae yake jinta a ran shi (abun daga Allah ne), furta mata Thanks yayi ta d'an yi murmushi sai kuma tace to shi bai ce mata ba still da d'an murmushi a fuskar shi yace ai yayi wannan tun da yazo garin su ta d'an tura mashi baki tace wannan ai dalili ne yasa ya fad'i mata kuma yanzu bata san ya take a wurin shi ba, shiru yay kawai yana kallonta don Maganar tata ta bayyana yarintarta a wurin shi don in bai sonta Maganar auren su zata d'ore ne, d'an yamutsa mashi fuska tayi tace ita bazai fad'i mata ba d'in,

"Not now" shine abunda taji ya fad'a ta gyad'a kai, cigaba da kallon juna sukai tana ta mashi murmushi shima fuskar shi a d'an sake can ya kai hannu ya shafi forehead d'in shi bayan ya ciro hannun ya d'an yi yar hamma, tambayar ta yay har yanzu jin muryar nashi bai isheta bane yana son yayi bacci yadda yay Maganar har saida ya bata dariya cikin wasa tace "ai bata isa na in ina jinta ban k'i ma mu kwana ba inata jinta" d'an wara ido yay ya tambayi is she serious ta d'aga mashi kai kafin tace ko ba zai iya kwana yana hira da ita ba , shiru ya d'an yi yana kallonta kafin yace to mi zai sa su kwana suna magana ai sai Maganan ma ta k'are tana yar dariya tace ba gashi yanzu ma sun d'auki lokaci suna hira ba kuma maganan bata k'are ba ai haka hiran love yake in ana yi ba'a gajiya, wani kalan kallo Yay mata yace waye ke yin love d'in ta nuna shi sannan ta nuna kanta wani irin kallo yay mata ya furta dama ashe bata ji ko tana dariya tace a'a ita tana ji ai ba k'arya tayi ba love d'in suke taga ya d'an girgiza kai slowly yace shi bai yin love da yarinya jin Haka yasa ta tura mashi baki kaman zatayi kuka tace Don Allah ita ya daina ce mata yarinya kawai sai gani tay ya saki yar dariya har dimple d'in shi ya d'an lotsa dama ya fahimci bata son ya kira ta da yarinya, bin shi tayi da kallo ko k'yaftawa bata yi can ta furta mashi dariya yana k'ara mashi kyau sosae kawai sai gani tayi ya d'aure fuskar yace ta fara raina shi ko ganin yadda yayi Maganar ne yasa da sauri ta girgiza mashi kai tace "taya zan raina ka bacin kai mutum ne mai girma da daraja a wurina wanda yay man alfarmar da ban ta6a zaton zan samu irinta ba a rayuwata, kullum ina son in gode maka amman na rasa taya zan hakan don Kalmar Thank you isn't enough, but I promise you I will be a devoted wife to you, I will make sure I give you all the happiness a wife can give to her husband in sha Allah, ina baka hak'uri in Maganar dana yi ka d'auka raini ce ba haka bane wllh kawai ina jin dad'in in ka sake man muna magana tunda ba cika yi kake ba" yadda ta k'arasa Maganar kamar zata saki kuka, murmushi taga yayi tare da lumshe mata ido a hankali ya furta mata thanks tare da Fad'in yana mata wasa ne kawai, sosae taji dad'i tana ta murmushi tace to yayi mata fatan Allah ya bata ikon yi mashi abunda tace ya d'aga kai kafin yace hakan itama tace mashi thanks, sigh yay ya furta "My devoted wife pls allow me to sleep na gaji sosae" Dariya Fauzy ta saka jin abunda yace shima yar dariyar yayi tace mashi to ya kwanta saida safe Allah ya tsare mata shi harda cewa yayi mafarkinta ya d'aga mata kai ta d'an d'aga hannu tana mashi bye bye daga haka yay disconnect, bayan sun gama wayar d'age kanshi yay a jikin kan gado yana d'an murmushi wani irin nishad'i yake ji tunda yake hira irin haka da mata bai ta6a jin dad'in wata ba kamar wannan lokaci guda yaji ya k'osa su zama ma'aurata don ta kasance a kusa da shi, itama bayan sun gama fad'awa tay saman gado tana murmushin jin dad'i wani kalan nishad'i na ratsa dukkan jikinta don tunda take dashi basu ta6a yin hira ba haka, lumshe ido tay suffar shi na dawo mata nan ta fara imagination d'in sun zama ma'aurata can ta bud'e idanun da sauri tana yar dariya a fili ta shiga yin godiya ga Allah da wannan babbar ni'imar da yayi mata don ko a iya haka sanin Sameer d'in da tayi tasan ni'ima ce, tana ta tunane tunanen shi a haka bacci ya kwashe ta.

Washe gari Misalin k'arfe goma saura masu tafiya nata shiri, bayan Aunty Mareeya ta gama shiryawa ta nufi part d'in su Fatuu, lokacin data je har sunyi wankan safe ta koma ta kwanta saidai ba bacci take ba hira suke da Mino sai Aysha kanwarsu, da sallama ta shigo cikin Bedroom d'in Fatuu na ganinta ta yunk'ura ta tashi zaune tana fad'in sunanta ita kuma tana amsawa tana karasowa wurin gadon, a baki ta zauna Fuskar kowannen su da Murmushi su Mino suka gaishe da ita ta amsa tare da Fad'in har an shirya tace mata eh, gaishe da ita Fatuu tayi ta maido idonta kanta ta amsa tace har anyi wankan safe tace mata eh, kallon su Twins tayi dake cikin gadon su tace suma sun sha wanka suna ta bacci Fatuu tace eh sun sha wankan Kakar su Yadikko Aunty tace ah lalle dole suyi bacci ashe mata ce ta sulle su duk akai yar dariya, tunani Fatuu tay k'ilan ko Maganar da sukai ne tazo fad'i mata tunda dama tace sai tazo Abuja hakan yasa ta kalli Mino da fulatanci tace su d'an basu wuri tace to ta kamo hannun Aysha suka nufi hanyar fita, bayan fitar su ne Aunty Mareeya tace "Yauwa dama kamar kinsan magana nike son muyi duk da dai ma ba wata ta sirri bane ai kan Maganar da muka yi ta gidane, na kira Yayan mu yaje ya samu Baban mu sun tattauna, abunda ke faruwa Zarah gaskiya samun irin gidan da shi Sameer d'in zai so zai yi wuya a garin namu yawancin manyan gidaje duk masu su ne a ciki saidai za'a iya samun sabo wanda ba'a kammala ba sai a ida ginawa to amman irin wannan gaskiya sai a wajen gari haka, to yanzu dai shawarar da aka yanke itace wai ko kawai ayi renovating namu gidan tunda ba laifi d'an babba ne kuma gaskiya ginin shi mai kyau ne don da asali ginin k'asa ne irin na da d'in nan to a hankali lokacin Babanmu na aiki ya fara maida shi na bulon siminti zuwa lokacin daya aje aiki aka gama maida shi gaba d'aya na siminti kinga sai kawai a gyara a yi mashi dai irin adon zamani, kai Fatuu ta jinjina bayan ta gama tace "kuma hakan yayi Aunty Mareeya tunda kun saba da Unguwar gaskiya bazaku ji dad'in barinta ba kuma sai ma a maida shi na bene kawai" d'an zaro ido Aunty tay "na bene kuma Zarah, a'a ba sai anyi wannan uwar dawainiyar ba kar ma aga mun zaqe ki dai fad'a ma mijin naki yadda nace kar ai zancen benen nan" ta k'arasa tana yar dariya Fatun ma ita take yi tace ai da ta bari an fad'i hakan tunda dai yana da halin Aunty Mareeyar ta ce "ke dai kada ayi Maganar benen nan tawajena kinga sun duba mana sosae ban ma fad'i maki ba jiya fa Her Excellency tayi magana dani tace ba sai anyi ma Fauziyya komai ba na aure iya ita suke buk'ata" waro ido tay tace don Allah Aunty tace mata Allah kuwa, sosae Fatuu taji dad'i ta shiga washe baki tana fad'in kamar irin yadda akai mata itama ba'ayi mata komai ba Aunty tace ai yawanci Kusan duk kaddarar su daya da Fauziyya shiyasa Allah ya had'a su Fatuu tace hakane tay fatan Allah ya nuna masu bikin Aunty tace "Amin ya Rabbi, ai wllh a k'agare nike da inga anyi bikin nan ai dole ma ne muci uwar sabada bayan mun yi godiya ga ubangiji" dariya sosae Fatuu ke yi, bayan ta tsagaita tace "wai Aunty ina wannan mayaudarin daya yaudari Fauzy ya kuwa san da Maganar zata yi aure?"

"Oho, wama yasan duniyar da yake nasan gaskiya bai san da Maganar ba don kinsan fa Babanmu ya hana a bud'e Maganar yace a bari sai komai ya tabbata amman yanzu nasan da an fara aikin gidan zaki ga abun ya bayyana" jinjina kai Fatuu tay tace zata so taga fuskar shi ranar daya ji Maganar Aunty tay dariya tace shegen k'ilan har ciwon zuciya sai ya kama shi,

"Yauwa ina son dama in yi maki magana kan gyaran jiki kinsan fa jinin haihuwa na lalata duk wani shiri na jiki don haka dole sai kin k'ara yin sabon gyara" da sauri Fatuu tace eh dama tana son yi mata magana akan hakan, tambayar ta Aunty tay ai har yanzu jinin na zuwa ko tace mata eh ta sake tambayar ta yaushe zasu dawo Katsina ne tunda gama jarabawar su ta k'arshe ta taho tace sunyi magana da Ya Haisam kan hakan bada jimawa ba zata dawo Aunty tace "to abunda za'ai yanzu da mun koma zan tanadar maki masu kyau dama akwai wanda nasa za'a kawo ma Fauziyya daga Nijar don har yanzu ban fara bata komai ba Saboda kinsan in akwae k'ananun shekaru to ba buk'atar asha abubuwa sosae k'arshe yazo ya damu mutum shiyasa na bari sai gab da bikin amman dai ina bata nama mai romo sosae haka su fruit da fresh milk sosae nike sata tana ci Mino ma yakamata ace zuwa yanzu ana bata su sosae duk da dai bansan ko ana hakan ba amman dai zan ma gwaggo magana zuwa lokacin da za'a fara basu magungunan, shiri na musamman za'a yi masu in sha Allah",

Fatuu na dariya tace "shiyasa nike son ki Auntyn mu" itama dariyar take tace "ai bani da burin daya wuce inga kun kama mazajen ku gam gam wllh kuma ta wannan hanyar ne kawai in kuma aka had'a da biyayya ai magana ta k'are" kai Fatuu ta d'aga ta k'ara cewa "in dai kinga alamun ba nan kusa zaku koma ba to ki man magana sai in aiko maki dasu nan kema kuma sai ki dage da cin abubuwan dana lissafa kinga ma har twins d'in mu sun amfana suma tunda naga kaman kina da kyaun ruwan nono don cikin sati d'aya kinga Tubarkallah sun k'ara girma wllh" amsa mata tayi da to suka d'an k'ara yin hira kafin Aunty ta mik'e tace yadda sukai da Haisam sai ta sanar mata tace to in sha Allah yanzu bada dad'ewa bama zata yi mashi Maganar. Misalin k'arfe goma da rabi duk masu tafiya suka firfito lokacin tuni su Hajiya Zainab sun tafi harda Mahaifiyar su da yan'uwanta yan Ethiopia suka tafi can Nasarawa haka su Hajiya Maryam ma Farha harda musayar lambar waya ita da Fatuu don Hajiya saida ta k'ara masu fad'a da Nasiha kan rashin shirin da suke ta nuna masu duka duniyar nawa take, dama su Yadikko driver da ya kawo su ne zai mayar dasu shi dai Kamalu Katsina zai wuce dama da shirin hakan ya taho don sun gama magana da Kawu Amadu zai koma can shima yaci gaba da karatu Saboda yanata zama ba karatun tun bayan daya gama Secondary, yan d'aura ne suka fara tafiya gaba d'aya su Mom aka fito yi ma su gwaggo rakiya driver su Yadikko nan cikin harabar gidan ya shigo Haisam yaje bayan sun gaisa ya tambayi yadda aka yi dashi zai kawo su ya kuma maida su cikin washe baki driver d'in yace ai shi Abokin Mahaifin ita mai jego d'in ne to yadda sukai ya zuba mashi mai ne zai kawo su ya koma dasu sannan sai ya Sallame shi Haisam d'in ya tambaye shi nawa ne kud'in sallamar yanata washe baki yace mashi ai ko nawa ne aka bashi lafiya lou tunda dai duk abu na gida ne, kud'i masu yawa ya bashi yana ta godiya da sa Albarka sai daga baya ma ya gane shine Mijin inna wuron suma su Yadikkon saida ya basu kud'i wai susha ruwa a hanya su Yaya ana ta washe baki ana godiya, su Gwaggo ma saida ya basu kud'in dama da zasu zo saida ya tura ma Abbas da Tk kud'in mai, Gwaggo da Aunty Mareeya suna ta ya barshi don Allah shida yay hidima yana murmushi yace masu ba wani abu, Nameer na lik'e da Mino sai shagwaba yake mata wai dama ace Shikenan tazo bazata koma ba tana ta murmushi ita kanta ji take kamar kar su rabu ba kamar yanzu da taga ya wani k'ara yin Fresh, sallama suka shiga yi ma juna su Mom da Hajiya nata masu godiya da Addu'ar Allah ya bar zumunci duk suka shishshige cikin Mota Abbas ne ya d'an d'aga murya yace ma Mino in sun gama shan soyayyar ta taho su tafi in kuma su barta anan to su Mom duk sukai dariya Hajiya tace ai in sun bartan daidai kenan kawai sai a d'aura aure ya wuce da ita ba shikenan ba ita kuwa Mino kunya ce ta kamata, daga baya dai duk suka shishshiga ana ta d'aga ma juna hannu a tare Motocin suka tafi sai fatan Allah ya kai su lafiya sai kuma an sake had'uwa bikin su Mino da Aunty Laila.

Misalin k'arfe biyun rana lokacin Aunty ta dawo daga aiki don bata nan yan tafiya suka tafi bayan ta kimtsa ta nufi part d'in su Fatuu don duk su Aunty Laila na can harda Fanan anan ma suka ci abincin rana gaba dayansu don yaran gidan k'in zuwa School sukai wai gajiyar suna bata sake su ba, tana shiga duk suka yi mata Welcome kowa yana murmushi haka itama shi take masu ta nufi kujera tana ruk'e da wasu Manyan fararen ledoji masu d'auke da tambari ta zauna Jidderh ce ta tambayeta ta zubo mata Abinci tace eh ba da yawa ba ta d'an ci wani a wurin aiki tace to

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login