Showing 306001 words to 309000 words out of 512766 words

Chapter 103 - Asanadin Makwabtaka Book 3 Hausa Novel Complete

Unknown   

27 Dec 2024

1542

d'aukar masu guda ukku daga haka gwaggo tace to a bashshi,

kallon Fauzy Fatuu tayi tace mata ta d'auki duk abunda take so da sauri ta girgiza mata kai tace wllh ba abunda zata d'auka duk uwar hidimar da akai dasu ga anko mai tsada har kala biyu gwaggo dai murmushi kawae take, madaidaicin akwati aka d'auko bayan an kwashe kayan cikin shi an maida cikin wani suka zuba kayan da suka d'aukar a cikin shi har Fauzy zata rufe Fatuu ta dakatar da ita, wani akwati ta nuna mata tace don Allah ta d'aukko mata, bayan ta jawo mata shi tasa ta bud'e, had'add'un dogayen riguna ne a ciki duk a Dubai aka siyo su Fatuu ta kai hannu ta ciro wata army green mai shegen kyau tasha adon stones, bayan ta saka cikin kayan tace ma Fauzy ta rufe, maida akwatunan sukai yadda suke da, tambayar gwaggo Fatuu tay jakarta da ta zuba kud'in da ta samu ranar Walima dama ita taba ajiya, bayan ta d'aukko mata ta bud'eta cikinta dankam take da kud'i, envelope d'in da Alhaji Lawal ya bata ta fiddo ta bud'e, kud'i ne a ciki bandir din yan dubu na dubu d'ari, maida su tay cikin envelope d'in ta d'auketa bayan ta rufe jakar ta mik'a ma gwaggo tace to ita da zasu tafi, ce mata tay ta tafin mata da ita kawae ba abunda zata yi da su don tana da kud'i sosae a account d'in ta.

A tare suka fito daga cikin d'akin Fauzy na janye da akwatin kayan, a parlor suka iske Hajiya zaune tace ma Fatuu ta k'yale su suje ita ta koma taje ta natsu wuri guda a marairaice tace mata tana son yin sallama dasu ne, lokacin da suka isa part d'in bayan gaba d'aya a parlor suka iske su don Abbas ya kira Feenah yace bada jimawa ba zasu tafi su zama cikin shiri, gaishe gaishe aka shiga yi ana k'ara yi ma Fatuu ya jiki bayan sun gama gwaggo tasa Fauzy ta bud'e akwatun, fiddo kayan su Yadikko tay harda turarurrukan su Ard'o ta nufi d'akin da suke don ta kai masu, suma na nan parlon Fauzy ta shiga fiddo na kowa tana bashi farko duk cewa sukai don Allah a bashshi banda duk uwar Hidimar da akai masu, saida gwaggo ta fito ta saka baki sannan suka amsa suna ta godiya da Addu'oi cike da Farinciki su Yadikko ma duk suka fito suna nuna masu nasu sai murna suke karma su Yaya da innar Altine su ji sam sun kasa rufe baki, fiddo kud'in da Fatuu tazo dasu tay ta shiga ba kowa dubu biyar biyar Haulat dae dubu talatin ta bata harda wanda zata yi kud'in Motar komawa Niger, nan fa parlor ya kacame anata farinciki Aunty Mareeya harda cewa in haka ake yin biki ai ba abunda zai hanata zuwa in dai ba ciwo ya kai ciwo ba duk aka sa dariya dama tun ran Asabar duk aka basu abubuwan da akayi na bikin, fakaitar idanun mutane Fatuu tay ta d'aukko trolley d'in Fauzy dake a cikin parlon, bud'e shi tay ta d'aukko jallabiyar da ta sako cikin kayan ta tura acikin akwatin kayan Fauzy data lura saboda a kusa da ita take tana niyyar yin Magana ta hau yi mata magiyar kar tace komai, wani kallo tay mata mai kamar harara Fatun ta saka dariya,

Gaba d'aya tare suka fito lokacin wuraren k'arfe goma yan Katsina da yan Adamawa harda wasu yan Daura, a gaban Entry Hall aka jere Motocin gaba d'aya duk an fito da yan tafiya da yan rakiya su Hajiya, Mom, Laila, Fanan, nan aka shiga yin bankwana Haisam da Abbas na daga can gefe sun jingina da Motar Abbas haka su Kawu Amadu da Tk da Kamalu ma duk suna gefe, Jidderh Saboda tafiyar tasu dama tak'i zuwa School Aunty dae ta tafi wurin aiki dama tayi sallama dasu kafin ta tafi Fatuu ji take kamar a tafi da ita, had'a ido sukai da Haisam ta yamutsa fuska ya saki murmushi don ya gane mi take nufi, Mino ma sai kallon love suke ita da Nameer suna sakar ma juna murmushi, Dad ne ya fito tare dasu Ard'o Fatuu ta nufe su ta gaishe su duk suka amsa Dad yay mata ya karfin jiki tace Alhamdulillah, kallon Baffan ta dake ta sakar mata murmushi tay itama murmushin take mashi sun kasa ce ma juna komai, kud'i Dad ya fiddo ya shiga raba ma duk masu tafiya aka hau godiya daga baya suka fara shiga cikin Motocin bayan an sassaka kayan su, d'aga ma juna hannu suka shiga yi kamar kar a rabu a Kusan tare duk suka tashi Motocin suna ta cigaba da d'aga ma juna hannu a haka suka tafi sai fatan Allah yasa a sauka lafiya, tsaye Fatuu tay idanun ta sun ciko da k'walla gaba d'aya har kewar su ta fara kamata, bayan barin Motocin aka tuk'o wadda Senator zai hau ta tsaya a gaban wurin dama a shirye yake, sallama yay da iyalin nashi duk sukai mashi sai ya dawo bayan an bud'e mashi k'opa ya shiga suka tafi, Haisam ne ya matso gaban Fatuu suka had'a ido a shagwabe ta tura mashi baki yay murmushi, Hajiya ce tace mata to suje ya kai hannu ya kamo hannunta duk kunya ta kamata suka nufi cikin gidan........

87

.......Alhamdulillah matafiya duk anyi waya da su sun isa lafiya gaba d'aya sai fatan Allah ya huta gajiya, bayan sallar isha Fatuu ta gama sallar tana zaune a saman gado jikinta sanye da voile material pink d'inkin riga da skirt tayi d'aurin kallabi mai kyau daga cikin kayan lefenta ne yayi mata kyau sosae, ruk'e take da wayarta tana bin chat d'in group d'in su na School da ake hirar komawa Makarantar bayan sun gama taya Fatuun murna data tura masu pics d'in bikin nata da akai,

Haisam ne ya shigo cikin d'akin jin sallama yasa ta d'aga ido ta kallo shi, k'arasowa yay ciki idon shi akanta suna ma juna murmushi, ta gefen inda take ya zagaya ya zauna a bakin gadon ta gaishe dashi ya jinjina mata kai, hannu ya kai ya shafi fuskar ta yace "Ya jikin ki?" tana murmushi tace mashi itafa lafiya lou take jin ta wllh, kai ya d'aga sai kuma yace to ya Baby d'in su tace yana nan lafiya bacci yake yanzu amman d'azun da suna fira yace ta gaishe mashi da Dad, dariya duk sukai yace Baby Boy ne kenan tace tana dai Fata amman duk wanda ta samu tana so ya jinjina mata kai, tambayar shi tay shi mi ya fi so ta haifa tun kan ta rufe baki ya girgiza mata kai yace kamar yadda ta fad'a duk abunda ta haifa zai yi farinciki yana fatan Allah ya k'ara mata lafiya da Babyn yasa ta haihu lafiya tana ta murmushi ta amsa da Amin, hannu ya kai ya jawota jikin shi da sauri ta shiga k'ok'arin kwacewa yay mata wani kallo, d'an yamutsa fuska tay tace mashi Mom take tsoron ta gan su haka, d'age mata gira yay yace in ta gan sun sunyi laifi ne a shagwa6e tace "to ai Hubby da kunya fa ka manta jinya nike" yadda tay Maganar ne yasa shi yin yar dariya har hak'oran shi suka bayyana, jawota yay sosae ya rungumeta a wurin kunnanta ya rad'a mata to Mom d'in bata nan sun fita da Aunty, shiru tay ta d'an ji hankalinta ya kwanta dama lokacin da ta gama sallar isha tana zaune kan prayer mat tana Addu'a taga shigowar ta bata jima ba kuma ta fita bayan ta yafa mayafi, tun bata saki jiki ba har dai ta saki ganin shi ba abunda ya dame shi, Maganar School tay mashi tace ran Wednesday suke komawa, jinjina mata kai yay yace ta bari zasu koma taci gaba da zuwa amman ba yanzu ba sai an d'an k'ara lokaci in ta kama sai ayi Magana can school d'in ta d'aga mashi kai, Wayar shi dake ruk'e a d'ayan hannun shi ya d'ago ya fara daddana ta idon ta akan Wayar, hotunan wasu Motoci ya fara nuna mata tana ta kallo har ya kai k'arshe guda Kusan Goma ne, maida idon shi kan Fatuu yay yace ta gan su ta d'ago ta kalle shi tace eh, tambayar ta yay wacce tayi mata da alamun rashin Fahimta tace bata gane abunda yake nufi ba, shiru ya d'an yi tana ta kallon shi kafin taji yace yana nufin tay choosing wadda take so a ciki, waro ido Fatuu tay da tsananin mamaki take kallon shi shima kallon nata yake da murmushi,

"Amman Saboda mi to zan za6a" ta tambaya da alamun mamaki yace mata Saboda za'a kawo mata ne, k'ara zaro ido tay ta furta "Motar!" Kai ya d'aga mata had'i da d'an lumshe ido a shagwabe tace "ni dai Hubby a'a ka barshi ba duk akwae Motoci ba har acan gidan Hajiya ma" kallon ta kawai yake sam bai yi mamakin jin hakan ba don yasan halin ta kan hakan bata son ya kashe kud'in shi yay mata abu in bai zama dole ba gashi kuma ita ba tambayar shi abu take ba, ganin kallon da yake mata yasa ta fara tura mashi baki ya kai hannu ya d'an matse bakin ta yi d'an sauti alamun taji zafi, sigh yay yace shima kyauta ce zai bata kan wadda ta bashi cike da shagwaba tace to ai ita ba ita ta bashi ba ko Allah ne ya bashi, yana murmushi yace yasan da wannan amman ai a jikinta yake ko, yamutsa fuska ta shiga yi yana murmushi yace mata wannan ce kyauta ta farko da ya fara bata a matsayin su na ma'aurata dole sai ta amsa tace ba ga uban lefen da yayi mata ba nan, ce mata yay Wannan ai ba gift bane tunda ya zama al'ada kuma bashi kadae yayi shi ba, sai shagwaba take mashi kanta na a kan shoulder en shi da alama ma ta manta da inda suke, bud'e mata Motocin yay yace in bata za6a ba bazai ji dad'i ba yayi zaton zatai murna ne ya bata gift in kuma wannan bai mata ba ta fad'i duk abunda take so, da sauri ta kai hannu ta tallabo gefen fuskar shi tace "a'a Hubby naji dad'i wllh kawae naga kaman wannan kyautar tayi girma ne kuma naga akwae Motocin" ce mata yay to su motocin dake akwae d'in nata ne ta girgiza mashi kai yace to yanzu ta za6a sai ya zama itama tana da nata ko, kai ta d'aga mashi tana murmushi har ta maida idanunta akan Motocin sai kuma ta d'ago da sauri tace "amman Aunty Fanan fa?" d'an murmushin gefe yay ya furta banda ita, waro ido tay sai kuma ta hau girgiza kai tace a'a don Allah bazata ji dad'i ba wllh itama gaskiya a bata yana murmushi ya furta Justice for Fanan da sauri ta d'aga kai tace eh, sosae yaji dad'in hakan data yi ta tabbatar mashi da Maganar da tayi mashi na zata taimaka mashi yayi masu Adalci, ce mata yay kada ta damu Fanan ma nada Mota a can Us ya siya mata ba'a dad'e ba,

"Da gaske?" ta d'age mashi gira shiru yay yana kallon ta, sake ce mashi tay da gaske yake ya siya mata yana murmushi yace "da k'arya" dariya ta saki don tasan wasa yake itama hakanan jan magana yasa ta tambayi da gasken tunda tasan bazai mata k'arya ba, maida idonta tay kan Screen d'in tace to bari ta za6a, gaba d'aya ta rud'e don kowacce ta had'u kama daga Camry, Hyundai, Corolla Mercedes da sauran su, wata Jeep ya bud'e har zai wuce da sauri tace mashi ya tsaya, k'ura ido tay tana kallon ta sosae ta burgeta don dama tana son Mota Jeep kuma tana son farar Mota to itama Jeep d'in fara ce, ganin tana ta kallon ta yasa shi ce mata tayi mata, jimm tay sai kuma ta d'aga ido ta kalle shi ya d'age mata gira alamar ta amsa mashi, kai ta d'aga ya furta Ok da d'an murmushi sai kuma da sauri Fatun tace "amman nawa take?" shiru kamar ba zai yi magana ba slowly yace tunda tayi mata Shikenan ai mi zatai da kud'in ta, a shagwabe tace ita dai ya fad'i mata gaskiya in mutum zai siya Mota ba sai an fad'i mashi kudin ba, dariya yay bai san ranar da zata daina wauta ba, ce mata yay to ita siya zata yi ne,

"eh ai tunda kai zaka siya man to kaman ni zan siya ko" ta k'are Maganar ta d'an tura mashi baki, d'an lumshe mata ido yay ba zato taga ya matso da face d'in shi yay pecking lips d'in nata ta d'an waro ido ya d'ago yana murmushi, rigimar sai ya fad'i mata kud'in Motar taci gaba da yi ya tambayi to mi zatai wai in taji kud'in tace hakanan take so taji, still murmushi yake wasu abubuwan ta kaman Hajiya, ya gane wai wayo take son yi mashi in taji tayi kud'i sosae tace bata son ta, girgiza mata kai yay yace an gama Magana ba sai taji ba shima ba siya yayi ba, k'una k'uni ta fara tana ita dae Allah bata yarda ba tunda shi yace ta za6a to ya fad'i mata kud'in, gaba d'aya yadda take mashi ta tafi da shi sai kallon ta yake dama d'an kwana biyun nan har ya fara jin kewar ta a tare da shi, ganin irin kallon da yake mata ne yasa ta dakata da abunda take suka zuba ma juna ido breathing d'in su na had'uwa, sun d'an d'auki lokaci a haka fuskar Fatuu da d'an murmushi kawai sai gani tay ya matso da fuskar shi ya had'e da tata, had'e lips d'in su yay farko fara k'ok'arin kwacewa tay amman yak'i bata dama daga baya kuma ta biye mashi don itama tayi kewar hakan,

"To, to da kyau, sannun ku da aiki" kaman daga sama suka ji an fad'i hakan gaba d'aya sai da suka d'an firgita da sauri Fatuu ta janye jikinta daga nashi a tare suka juya don ganin mai Maganar, Hajiya ce ta shigo tana dogara sandar ta jikinta sanye da kaftan ta atamfa tayi d'aurin kallabi irin nasu na manya idanunta sanye cikin glasses, wata irin kunya ce ta rufe Fatuu da sauri ta sunnar da kanta duk da bata san ko taga abunda suke ba don sun ba kopar shigowar baya to amman gaba d'aya tana a jikin shi ya tallabe ta a ranta ta raya da k'yar in bata ga abunda yake matan ba, idon Haisam a kanta har ta k'araso ciki ta tsaya daga gaban su ta d'aure Fuska, murmushi yay ya gaishe da ita ta wurga mashi harara tace "Yanzu miye wannan d'in, kasan halin da yarinyar nan take ciki amman shine bazaka iya hak'uri ka bari tabi dokar likita ba ta samu hutun da take buk'ata saboda tsabar jaraba, anya Haisam!" ta k'arasa Maganar ta d'an 6ata rai, still Murmushi yake ya d'an d'age mata gira yace "Yanzu nayi wani laifi ne" a fusace tace bata sani ba, yar dariya yay yace in dai hutu ne ai gashi tana hutawa ko, kwabe fuska tay ta jinjina kai tace eh tabbas ta gani hutawa take, maida idon ta tay kan Fatuu da tai tsumu tsumu kanta a k'asa ji take kaman ta nutse a wurin, ce mata tay ta tashi ta gama hutun anan don ba barin ta za'ai tayi yadda ya kamata ba, zuru da k'afafun ta tay still bata kalli Hajiyar ba ta mik'e, da sandarta tayi mata nuni da hanya tace su je, har zata tafi sai kuma ta dakata Hajiya ta tambayi ya akai k'asa k'asa tace zata d'auki kayanta ne, tambayar ta tay suna ina da k'yar ta d'an d'ago tay mata nuni da inda trolley d'in ta yake, nufar wurin tay tana dogara sandar, jawo shi ta shiga kokarin yi Haisam dake zaune yay yar dariya ya mik'e, wurin ta yaje yace ta kawo ya taimaka mata fuska a d'aure ta kalle shi tace bata so, hannu ya kai ya amshi akwatin ya fara ja Hajiyar ma ta fara tafiya da sauri Fatuu ta juya ta nufi k'opa sumi sumi,

Sun rigata zuwa bakin part d'in nata cikin d'an d'aga murya tace ma Haisam ya aje akwatin nan kar ya shigar mata d'aki ya kama gaban shi murmushi kawae yake ya shige dama ita Fatuu tuni ta shiga, tsaye tay a parlor yana shigowa suka had'a ido a tare suka saki yar dariya suna haka Hajiyar ta shigo da sauri Fatuu ta juyar da kanta, tambayar ta yay a ina za'a aje akwatin tace bata sani ba ya aje a duk inda ya ga dama tunda dai ya raina ta ai saida tace kar ya shigo amman ya shigo, shiru yay can kuma yace mata to tayi hak'uri don ya rage mata aiki ne kawai ba wani abu ba, kaman bazata tanka mashi ba sai kuma tace to ta gode yaje kar kuma ya sake ta k'ara ganin k'afafun shi a part d'in ta, yana dariya yace ai wannan dole ne ya zata d'aukko mashi mata tace kuma kar yazo ai dole yazo ko don ya duba tafiyarta ko, hararar shi tay tace ko don fitina dai, maida idonta tay kan Fatuu dake kallon gefe tace ta wuce ta shiga cikin daki ta nufi hanyar shiga d'akin ba tare data kalle su ba, hannu Haisam ya kai zai d'auki akwatin yana fad'in bari ya shigar mata da shi aikuwa ta d'aga sandarta zata kwad'a mashi da sauri ya kauce yana dariya yace "Sweetheart yau ni zaki buga" fuska a d'aure tace ai bai fi k'arfin shi ba in dai bai fita ya bata wuri ba Allah zata bubbuga nashi ita, cewa yay Allah ya bata hak'uri bari ya fita ai duk abu mai sauk'i ne, saida safe yay mata a

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login