Showing 420001 words to 423000 words out of 512766 words

Chapter 141 - Asanadin Makwabtaka Book 3 Hausa Novel Complete

Unknown   

27 Dec 2024

1623

zuwa ta haihu ta kalli Haisam dake kallon su fuskarshi a sake tace daga yanzu su fara mata Addu'a ya jinjina kai, tattaunawa Fanan ta shiga yi da Doctor kan maganin daya kamata a bata wanda zai sa ta daina amai ta rinka cin Abinci haka su twins ma suma za'a basu wanda zai k'ara inganta lafiyar su Haisam ya tambayi yanzu zata iya cigaba da breastfeeding nasu doctor din yace k'warae ba wani abu taci gaba da basu koda har zuwa ta haihu ne kuma a rinƙa basu maganin da zai basu yay mashi godiya.

Bayan sun baro Asibitin tun akan hanya Fanan ta shiga kiran yan Nigeria su Hajiya da Mom ta sanar masu harda Gwaggo ma kowa yay mamakin jin samun cikin daga baya duk sukai Addu'oin Allah ya inganta ya raba lafiya. Sosae Fanan ke kulawa da Fatuu bayan da suka san da cikin haka su twins ma in dae tana gida bata je aiki ba ita ke duk wata ɗawainiya dasu dama tana kulawa dasu sosae yanzu sai ta k'ara don komai ita ke masu kama daga yin wanka shirya su basu Abinci yi masu wasa da sauransu haka Haisam ma in yana a gidan tare dashi ake masu komai koda Fatuu tayi yunƙurin yi masu wani abu sai suce ta bashshi ta huta duk da jikin nata da Sauk'i sosae iyakar ta shayar dasu sai kuma in suna zaune tare dasu ta d'auke su har tayi masu wasa, k'arshe ma Haisam cewa yay yakamata a samo masu nanny Saboda in basu nan ba sai ta rink'a wahalar kulawa dasu ba amma sai ta nuna mashi ba sai an samo ba tunda ba wani ciwo take ba zata iya wannan amman ya nuna ta bari dai a samo ganin hakan yake so yasa ta amince amman tace to ya bari tunda sun kusa tafiya biki in suka dawo sai a samu ya amince da hakan.

A kwana a tashi ba wuya a wurin Ubangiji, bikin su Nameer nata matsowa har ya rage saura sati ukku lokacin watan Fatuu biyu da sati guda a Us, a yadda sukai da Haisam in ya rage saura Sati biyu zata tafi shi kuma sai ana saura sati d'aya zasu taho shi da Fanan, gudunmawar miliyan biyu ya bata yace in basu isa ba tayi mashi magana cike da nuna farinciki ta nuna mashi sun isa har ma sun yi yawa, a yadda sukai da gwaggo bayan ta kirata kan Maganar kayan ɗaki ce mata tayi tana ganin kawai za'a siya mata ne ready made har ma tayi ma Aunty Mareeya magana kan hakan tace in an tashi siya akwae inda zata kai su suna da kaya masu kyau wanda za'a siya ma Minon, Fatuu taji dad'in jin hakan gaba d'aya gudunmawar da Haisam ya bata ta tura ma gwaggo tace saura tata in tazo Gwaggon tace wannan uban kuɗi haka da ɗanta ya bada anya basu yi yawa ba Fatuu na yar dariya tace mata a haka ma cewa yay in basu isa ba tayi magana ya ƙara da sauri gwaggo tace don Allah kada ta ƙara tambayar shi ko Naira wannan ai Kusan ma shi zai mata kayan ɗakin, tambayarta Fatuu tayi kamar ya za'a mata kayan gwaggo tace wai da ita a tunaninta ayi mata saitin gado da kujeru masu kyau wanda da an gani ansan masu kud'i ne tunda Baffan su ma sunyi Magana kan kayan ɗakin ta nuna mashi ya turo kuɗi kawai a siya sai duk a haɗa a siya mata, cewa Fatuu tay gaskiya kamata yay ayi mata komai set biyu kujerun da gadon don tasan gidan da za'a kaita babba ne alabashshi ko sai a siya set ɗaya masu kuɗi sosae sai ɗayan koda wanda basu kai su kuɗi ba Gwaggon tace to hakan ma bari in aka harhaɗa kuɗin sai aga kaman ya za'a siya mata don itama tana son a yi mata kaya sosae tunda ita ba'a yi mata komai ba Fatun tace komai kenan sai tazo sai suje a siya in sha Allah ba abunda zai gagara bane, itama Gwaggon tace in sha Allah nan take faɗi mata Hajiya tayi mata magana kan inda za'a ɗaura aure sun roƙi alfarmar in ba takura a ɗaura a nan Katsina sai a haɗa da na Laila a ɗaura gaba ɗaya anan sai a tura Mota can Adamawa ta ɗaukko masu zuwa ɗaurin auren nan don in akace ayi acan sannan ayi na Laila a Abuja za'a takura mutane don zirga zirgar zata yi yawa to ta kira Baffansu kan hakan shima yayi magana da yan'uwanshi duk sun amince da hakan shi Arɗo ma ance ba lalle yazo ba don bai jin daɗi Fatuu ta tambayi abunda ke damun shi tace mata kawai harda tsufa wai jikin nashi ne bai jin daɗin shi, fatan Allah ya bashi lafiya Fatuu tayi kafin suyi sallama Gwaggo ta tambayi ina Y'ay'anta Fatun tace gasu can wurin Aunty Fanan wai tafiya take koya masu, yar dariya gwaggo tayi tace da wuri haka Fatun tace eh wai daga taga sun fara tsayuwa shine ta fara koya masu Gwaggo na dariya tace ina ruwan ɗiyarta tana dai kula da yaran sosae Fatun tace sosae don yanzu har aiki take tafiya dasu ta bada su wurin raino a can har makaranta aka so saka su amman ta hana wai ai a wurin rainon ana koya masu abunda ake koyawa a Makarantar, da alamun mamaki gwaggo tace "wace irin Makaranta kuma yaran da basu wuce wata bakwae ba" yar dariya Fatuu tayi tace mata su nan haka suke yi kamar wurin raino ne to sai a rinƙa nuna masu abubuwa don su taso sun sani gwaggon tace ta gane aikuwa bari itama tazo ta koma Makaranta ko ta ƙara sanin abubuwa kada suzo su ƙureta harda ma turanci zata koyo, Fatuu nata Dariya itama gwaggon Dariyar take daga baya ta tambayeta ya jikin nata ta bata amsa da Alhamdulillah tace badai ta laulayi sosae ko Fatun tace mata eh ai maganin da take sha kullum yana hana ta yin amai ko tashin zuciya lafiya lau take cin Abinci saidai wani lokacin tana jin kasala taita kwanciya sai kuma ciwon kai da take yi wani lokacin shima, Addu'ar Allah ya inganta ya sauketa lafiya gwaggon tayi Fatuu na murmushi tace "Amin ya rabbi, Allah ya amsa gwaggota mahaifiyata, ina tsananin son ki da dukkan zuciyata" wani irin murmushin daɗi gwaggo tayi itama tace "nima ina ƙaunar ki autata Fateema, ina roƙon Allah ya ƙara ma rayuwar ki albarka data zuriyar ki ya jiƙan Mahaifiyar ki" wani irin lumshe ido Fatuu tayi nan da nan idanunta suka ciko da kwalla don a lokacin nan koda yaushe Mahaifiyarta na a ranta sosae take jin maraicinta tana jin inama ace tana raye rayuwarta tayi albarka haka, jin tayi shiru yasa gwaggo kiran sunanta ta amsa a hankali tana jin yanayin muryar tata ta gane kuka take, itama zuciyarta karyewa tayi abubuwa suka fara mata yawo a rai tay ƙarfin halin ce ma Fatuu ta daina Kuka tayi mata Addu'a in sha Allahu ta dace a sanyaye ta amsa da Allah yasa, kafin suyi sallama gwaggon tace in kusa Fanan take ta bata su gaisa tace to, bayan ta kai ma ta a Nursery ta sanar mata ga gwaggo zasu gaisa cike da nuna jin daɗi ta amsa cikin washe baki suka gaisa gwaggo tace ai an faɗi mata tana nan tana ta aikin koya tafiya Fanan d'in tay dariya tace eh so take su iya kafin su zo biki yadda in suka zo zasu je ko ina da ƙafafun su gwaggon tace lallai kam akwae aiki yanzu nan da sati guda kenan take son su iya tafiyar tana ta dariya tace eh itama gwaggon dariyar take tace to Allah ya taimaka ya bada sa'a ta amsa da Amin kafin suyi sallama harda kara ma Adam wayar wai yace mata Hello sai gashi yace ɗin cike da jin daɗi gwaggon ta shiga yi mashi magana da hausa tana tambayar yadda suke shida ɗan'uwan shi yay zuru yana zaro ido Fanan da Fatuu sai yar dariya suke ganin yadda yay ganin sunata dariya yasa shima yin dariyar gefen kumatun shi duk suka lotsa Madarar kyau abun sai dai ace tubarkalla, amsar wayar Fanan tay gwaggo tace ko basu yi masu magana da Hausa ne tace a'a suna yi masu Momynsu ma harda Fulatanci tana masu magana haka Dad d'in su ma yana masu larabci zasu taso suna jin yare hudu Gwaggo tace Masha Allah Allah yay masu albarka da sauri ta amsa da Amin da zasu yi sallama Fanan ɗin harda cewa "We love you so much granny" gwaggo na murmushi da hausa tace "nima ina son ku Y'ayana, Allah ya ƙara ma rayuwar ku albarka ya ƙara haɗa kan ku ya kauda idon maƙiya da mahassada ya kare ku daga dukkan sharri" cike da jin daɗi Fanan ta amsa harda lumshe ido daga baya ta ba Fatuu wayar don suyi sallama.

Shirye shiryen biki nata kankama a dukkan 6angarorin angwaye da amaren, Bayan sati guda Fatuu ta taho da wata babbar Mata da zata zo Kano harda iyalinta Haisam ya haɗasu don su taimaka mata da su twins dama damuwar shi kenan yadda zata yi dasu shiyasa ma bata wani kwaso kaya ba iya ɗan babban trolley ne da yar jaka sauran sai zasu zo su taho mata dasu, bayan sun iso Kano Matar tace mata in ba jirgin da zai je Katsina yanzu sai su tafi gidanta kafin lokacin tafiyar yayi Fatuu na murmushi tace mata ai da Haisam ya siya mata ticket online akwae wanda zai tashi bada daɗewa ba yaran Matar suka shiga faɗin wayyo ba haka suka so ba sun so su bisu gidansu don basu gaji da ganin su twins ba ita dai Fatuu murmushi kawai take, itama Matar da wani matashin mutum da zai tafi Katsina ta haɗa su don ya taimaka mata shima a first class zai zauna inda Fatun zata zauna, lokacin Haisam ya kira don yaji in sun sauka Fatuu taba Matar waya sukai magana sosae yayi mata godiya tana ta fara'a irin tasu ta manyan Hajiyoyi tace ai ba komai duk yima kaine tana fatan wata rana in yazo ƙasar zai kawo mata su yace in sha Allah daga baya ta sanar dashi itama ta damƙa su a hannun wani da zasu zauna tare don ta bincika bata samu mace da zata zauna anan ba yace to ba komai ya ƙara mata Godiya kafin sukai sallama, Wuraren karfe sha biyu na rana suka sauka Katsina, cike da Farinciki su Gwaggo da kawu Amadu da Amarya Mino sai Tk daya kai su suka tarbe ta basu zo da Kamalu ba shi Kawu Amadu ya baro ma shago, kowa yay mamakin ganin yadda Fatuu ta canza har sun kasa rufe bakunansu gaba ɗaya hutu ya zauna mata sosae tayi 6ul6ul da ita ga skin ɗinta ta ƙara mulkewa ta ƙara haske in tayi dariya abun gwanin burgewa ga cikinta har ya ɗan fito, su Twins kam abun ba'a magana su wannan tun a jirgi aketa santin su, sai so suke su ɗauke su amman sun ƙi yarda dama Adam ne me ɗan yarda a ɗauke shi shima sai yaga Fatun na a kusa, da ƙyar ya yarda Mino ta ɗauke shi daga wurin mutumin da ya ruƙe shi a jirgi sai faman ta6e baki yake zai yi kuka Fatuu ta shiga rarrashinshi da turanci tana ce mashi itama Minon Mom ɗin shi ce, shi dai Abie na liƙe da ita da alama ma tsoronsu yake don har fuskar shi ta nuna ya waro ido tubarkalla sai bin su da kallo yake, Sosae su gwaggo sukai ma mutumin godiya yana murmushi ya nuna masu ba komai kafin sukai sallama ya tafi, bayan sun fito wurin da aka parker Motar su ukku suka shiga baya kawu Amadu ne yanzu zai tuƙa Motar don ya iya bayan tafiyar Fatuun Tk ya koya mashi da Motar tata tare da amincewarta, yana fara driving Fatuu ta shiga yaba mashi ganin har ya iya Tk dake gefen shi yace ai yanzu ba inda bai zuwa da mota, bayan sun bar Airport ɗin suna ta hira Fatuu ke tambayar Hajiya Tk na murmushi yace tana nan lafiya tana can tana jiran isowar su, lokacin da suka iso ƙopar gidansu tsayawa Fatuu tasa akai don ta gaisa da Yayanta Kamalu yana ganinta ya hau washe baki yace bari ya rufe shago yazo su ƙarasa gidan tare, a gaban Motar Tk ya matsa mashi suka tafi suna isa gate su officer suka taso suna masu sannu da zuwa daga baya aka buɗe masu gate suka shige, a gaban entrance ya parker Motar duk suka firfito lokacin Saude ta fito cikin washe baki ta nufo Fatuu itama tana ganinta ta fara mata murmushi tana zuwa ta ɗan rungumota tana mata sannu da zuwa aikuwa Abie na ganin haka ya fashe da kuka da sauri Aunty Saude ta saketa tana faɗin ashe ba'a ta6ata ta shiga ba shi haƙuri tana faɗin ai ta saketa to yay shiru ai kamar ma tana ƙara tunzura shi sai kukan yake ƙara yi ganin haka yasa Sauden cewa to ko dai tsoron baƙaƙen Mutane yake Gwaggo tace taga alama don tun ɗazu duk ya bi ya ƙanƙame Uwar tashi, ganin Abie ɗin na kuka yasa Adam shima fashewa da kukan dama ƙiris yake jira Mino ta matso dashi wurin Fatun don ta rarrashe shi, Hajiya ce ta fito tana dogara sandarta ta alfarma idanunta sanye cikin glasses ta nufo su tana faɗin ita dai tayi gajen haƙuri ta fito, ganin su twins na kuka yasa ta tambayi mi ya faru duk suke kuka Saude ta faɗi mata ta jinjina kai tana dariya tace aikuwa aiki ya same su in dai tsoron baƙaƙen mutane suke tunda ƙasar su suka zo duk akai dariya, gaishe da ita Fatuu tay ta amsa tana ta fara'a tay mata sannu da zuwa kafin tace to a shigo ciki a zauna yadda za'a gaisa sosae suka ce so ta kalli su twins da suka bita da ido tace masu barkansu da zuwa ƙasar baƙaƙen fata, tambayar ina mai gidan nata yake tay Fatuu ta nuna mata shi a hannun Mino tace wato ita kenan don tana fara ya yarda da ita duk sukai dariya, cikin gidan duk suka nufa a parlor aka zazzauna ana ƙara gaisawa da ƙara yi masu sannu da zuwa Hajiya ta tambayi Fatuu jikinta tana ta murmushi tace Alhamdulillah tay fatan Allah ƙara ingantawa ya sauketa lafiya ta amsa tare da su Saude, sake tambayar ya ta baro su Haisam Hajiyar tay tace lafiya lou duk suna gaishe su suna nan zuwa, Saude nata kallon Fatuu don komai tayi burgeta take can ta kasa haƙuri tace mata har ta canza sosae Hajiya tace ai dole yanayin ƙasa ba ɗaya ba, Maganar Abinci Hajiya tayi ma Fatuu tace gashi can an shirya akan table in kuma a kawo nan to tace eh a kawo nan cikin parlor Saude ta amsa da to ta miƙe, sallama gwaggo tayi masu Hajiya tace ta tsaya sai sun ci Abinci sannan, lafiyayyun Abinci da abun sha aka jere akan carpet duk Saude tay serving nasu abun yay kamar yar Walima har gwaggo na faɗin to kada kuma su cinye ma baƙi abinci Hajiya tace ai dama harda yan tarbar baƙin aka yi, a nutse suka fara cin abincin harda Hajiya a kan c-table aka ɗaura mata bayan ta fara ci tace ma Mino ta kawo mata Adam, kuka ya saka bayan ta kawo mata shi yana miƙa hannu alamar Mino ta ɗauke shi Hajiya ta shiga rarrashin shi tana faɗin "Haba mai gida yada tsoron Mata inata farincikin tarbarka sai kuma kaƙi yarda dani" su Gwaggo nata murmushi Hajiya ta kalli Fatuu tace "to wai ma yana fahimtata ko sai anyi turanci" amsa ta bata da eh suna gane hausa amma sun fi fahimta in akayi turanci, komawa Hajiya tayi tana rarrashin shi da turanci har ya fara yin shiru manyan idanun shi a kanta yana ta6e baki ita kuma tana ta faɗin yayi shiru shagwa6a66an maigida, lokacin da suka gama cin Abincin an kira Azahar Kawu Amadu da Tk suka tafi Masallaci gwaggo ma tayi ma Hajiya sallama su Fatuu da Mino suma suka fito don tafiya part ɗin su wanda tuni Saude ta gyara mata shi, bayan sallar la'asar lokacin Fatuu tayi wanka ta canza kaya haka su twins ma an yi masu wanka an canza masu kaya iri ɗaya suka tafi gidan Gwaggo, a can gidan ma anyi masu abincin tarbar su Fatuu tace sai anjima sai suci tunda yanzu basu jin yunwa suka shiga tattaunawa game da shirye shiryen bikin Minon nan Gwaggo ke sanar mata Abbas ya bata gudunmawar dubu ɗari biyu Fatuu taji daɗi tay godiya da Allah ya saka da Alkhairi, anan Haulat tazo ta iske Fatuu tsaf tsaf da ita tana sanye cikin doguwar rigar material mai kyau tayi rolling veil in ka ganta baka ta6a cewa ta ta6a aure tana ruƙe da hannun ɗiyarta lokacin data zo itama tsaf da ita an sa mata kaya masu kyau haka kanta ba laifi tana da gashi ma sha Allah, gaba ɗaya sunyi farincikin ganin juna Fatuu tace ai da tana niyyar zuwa gidansu bayan Magrib shiyasa bata kirata ba ta tambayi ya akai tasan ta dawo tace mata kawu Amadu ne ya kirata ya sanar mata, nan suka shiga yin hira itama saida ta tanka kan yadda Fatun ta canza tana dariya tace ai itama ta canza taji daɗin ganinta haka don da alama ta kwantar da hankalinta Haulat ɗin tace mata eh, duk yadda Haulat taso ta ɗauki su twins sun ƙi yarda kuma sun ƙi bari Fatuu itama ta ɗauki ɗiyar Haulat ɗin da tayi yunƙurin ɗaukarta sai su fashe da kuka abun ma sai ya zama abun dariya, tana nan har aka yi sallar Magrib bayan an gama ta tafi.

Washegari bayan sun gama yin breakfast ita

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login