Showing 342001 words to 345000 words out of 512766 words
Chapter 115 - Asanadin Makwabtaka Book 3 Hausa Novel Complete
Unknown
27 Dec 2024
1675
tambayar ta yay yaushe zai zo ya dawo da ita tay d'an Jim kafin tace to asaman mi zai zo ko ya bari ta dawo da sauri yace a'a indai zata kai dare to bazata yi driving ba, k'arshe Tk tace to ya turo sai ya dawo da ita yace Ok, ba kowa a cikin parlon lokacin da ta shiga yaran Aunty Mareeya na tahfiz, sallama ta tsaya tana yi a cikin parlon jin shiru yasa tayi tunanin k'ilan bacci suke ta nufi d'akin Fauzy, tura kopar tayi ta shiga da sallama tana shiga ta hango Fauzy kwance a saman gado tana facing ceiling ta d'age k'afafun ta, saida ta isa bakin gadon sannan ta ankare da ita da sauri ta kai hannu ta cire earpiece d'in dake a kunnanta ta tashi zaune jikinta sanye da jeans da shirt, waro ido tay alamar mamaki Fatun ta zauna a bakin gadon bayan ta aje basket din,
"Yaushe kika zo har ban ji shigowar ki ba?" Fauzy ta tambaya da alamun Mamaki, yar harararta Fatuu tay tace "Yaushe dama zaki ji na zo kin dad'e kunnuwa" dariya tay tayi mata sannu da zuwa Fatun ta amsa,
"Ya yi kyau Amaryar Ya Haisam Mom twins in sha Allah, wannan wanka haka kinga yadda kika had'u sai kikai kaman wata shuwa Arab wllh" yar dariya Fatuun tayi "godiya nike Amaryar Sameer in sha Allah" yanayin fuskar Fauzy ne ya canza tana d'an murmushi had'i da d'an ta6e baki Fatun tace ita da zata ce Allah ya yarda tay murmushi kawai,
"ina Ya Haisam d'in shi ya kawo ki?" Girgiza mata kai tay tace ita kad'ai tazo tace Napep ta hawo kenan, k'ara girgiza kai tay tace a Motar ta, da alamun mamaki Fauzy tace "inyee, kice hannun ki ya fad'a sosae" kai ta d'aga mata tana murmushi, shiru suka d'an yi duk suna d'an murmushi Fauzy na son tambayar ta yadda sukai da Haisam ta kasa can dai tay k'arfin halin ce mata ta tambayi Ya Haisam d'in tace mata eh,
"to ya kukai da shi ne?" Wani kallo mai kamar harara tayi mata tace "ba ke zan fad'i mawa ba wadda ta bani sak'on zan fad'i ma yadda mukai dashi" gyad'a kai tayi tace Allah ya bata hak'uri Fatun ta saki dariya, tambayar ta tayi Aunty Mareeya tace mata tana d'aki ita da mijinta k'ilan ko bacci suke tun bayan dai da suka ci Abinci kowa ya shige d'aki itama tayi baccin ta farka ne,
"ko in kira maki ita a waya ne?" Da sauri Fatuu tace a'a tunda ba yanzu zata tafi ba ta k'yale ta in ta fito sunyi Maganar tace to, kallon basket d'in data shigo dashi tay tace "k'awata mi muka samu haka?" tana murmushi tace mata alkubus d'in fulawa ne tayi, matsowa bakin gadon tayi ta kai hannu ta d'aukko basket d'in, a saman gadon ta d'aura shi kafin ta kai hannu ta bud'e babbar Warmer d'in, sosae Alkubus d'in yayi kyau ya bada shape d'in robobin da tayi amfani dasu wurin yi, bud'e d'ayar warmer d'in tay nan miya ce da ta ji had'i tayi kitif tasha ganda mai had'e da tsoka sai uban k'amshi ke tashi, jinjina kai Fauzy tayi tana murmushi tace "Abinci mai sunan Abinci dai na a Warmers d'in yan gayu" yar dariya Fatuu tay tace "su ku kenan",
Fauzy tace ina ai su ba yan gayu bane, rufe Warmers d'in tay ta maido basket d'in k'asa bayan ta aje ta d'ago Fatuu tace bazata ci ba tace zata ci bari cikinta ya d'an k'ara fad'awa yadda zata yi mashi cin mutunci ta d'aga mata kai, hira suka shiga yi farko kan Sameer ne Fauzy na bayyana mata abunda take tunani game da ba sonta yake ba kawai hakanan zai aure ta in ma an amince mashi kenan ita kuma Fatun tana nuna mata bata tunanin hakan daga baya suka dawo hirar karatun su, suna haka aka fara kiran sallar la'asar bayan d'an wani lokaci Fatuu ta mik'e don tayi salla, cire nad'in lifaya d'in tayi ya rage doguwar rigar ce a jikinta Fauzy dake kallon ta tace "Ma sha Allah abu dai sai k'ara girma yake, kinsan har na k'osa inga Babyn ku don nasan dole zai yi ko zata yi ruwan kyau wllh" dariya kawai Fatuu tayi Fauzyn ta k'ara cewa Allah dai ya raba lafiya tace Amin ya Rabbi, toilet ta nufa idon Fauzy a kanta tana magana kan yadda hips d'in ta suma suka k'ara bud'ewa, bayan tayo Alwalar ta fito ganin Fauzyn bata da niyyar tashi yasa tace mata ita bazata yi sallar bane ta d'aga mata tace "tawa ta kai tuni" yar dariya Fatuu dake tsaye tayi tace yaushe rabonta da tace bata salla tun bayan da ta samu ciki Fauzy tace dama ita da period yanzu ai sai bayan ta haihu in kuma tana daga cikin Matan da basu yi ne in suna shayarwa to har sai ta yaye bayan na haihuwa ya d'auke ta d'aga mata kai, Hijab tasa Fauzyn ta bata bayan ta shimfid'a mata abun salla ta kabbara, nufar k'opa Fauzy tayi ta fita bada jimawa ba sai gata ta dawo ruk'e da plate ta duk'a a gaban basket d'in ta fara zuba alkubus d'in, komawa tay saman gado ta fara ci,
"Wllh k'awata ba zancen santi ba kin bala'en iya girki, yanzu dai ji yadda wannan alkubus d'in yayi dad'i sai kace na alkama ne wllh, wai don Allah ya akai kika iya sarrafa Abinci ne Allah sau da yawa ina mamakin hakan acikin rai na" ta k'arasa tare da tura tsokar nama idonta akan Fatuu data sallame salla tana kallonta da murmushi,
"wurin gwaggo da Aunty Saude na koya na kuma k'ara da tawa fasahar, in kina so ki zo in koya maki ki rink'a yi ma Angon ki Sameer yadda zaki kama mana shi da kyau" tana dariya tace wannan wane irin Abinci ne bai ci ai tasan dole yana cin masu dad'i Fatuu tace to ai itama Hubby d'inta na cin masu dad'in amman a haka yake santin nata duk in tayi hakan ai ba hujja bace da zata ce bazata k'ara koyan yadda zata rink'a yin Abinci mai dad'i ba, sosae Maganar taba Fauzy dariya tace sai kace ta ga anyi auren nasu Fatun tace ai in sha Allahu ma za'a yi Sameer bai da wata mata sai ita da yardar Allah, shiru tay don bata san mi zata ce mata ba gashi tak'i ta fad'i mata yadda sukai da Haisam,
"Wai Fauziyya ko Zarah ta zo....." Kaman daga sama suka ji muryar Aunty Mareeya tana fad'in hakan, had'a idon da sukai da Fatuu data juyo tana kallon ta yasa bata k'arasa Maganar ba ta d'an waro ido alamar mamaki, k'arasa shigowa tay ta nufi bakin gado ta zauna idon ta akan Fatuu dake ta mata murmushi tace "yar gidana yaushe kika zo ban sani ba sai yanzu da Abban su Hanif ya dawo daga Masallaci yake man Maganar Motar da aka parker a waje saitin gidan nan naje na lek'o ta ina gani nace wannan ai Motar Zarah ce?" Gaishe da ita ta fara yi kafin tace mata tun d'azu tazo Fauzy tace mata tana bacci, kallon Fauzy dake ta cin Alkubus tay ta d'an harareta "maimakon kije ki fad'i man tazo" yar dariya tay tace to tana tare da mijinta ya zata je mata d'aki, "to uban me ake a d'akin da bazaki je ba ko yau kika fara zuwa" dariya suka saki harda Fatuu Fauzyn tace "uhmm nidai ai ban ce wani abu ba ko nayi tunanin ko kuna bacci ne kuma da har zan kira ki ita tace tunda ba tafiya zata yi ba in k'yale ki gata nan ki tambaye ta" tsoki ta buga still dariya Fauzy ke yi tace mata ga Alkubus nan Zarah ta kawo masu ta jinjina kai, maido idon ta kan Fatuu tay tayi mata godiya ta tambayi mijin nata ya dawo lafiya dasu Hajiya da gwaggo duk ta amsa mata, mik'ewa tayi ta cire hijab d'in tana cikin ninketa Aunty dake kallonta tace "yar gidana abun Alheri dai sai k'ara girma yake ma sha Allah, amman ya fara motsi kuwa?" tana dariya tace mata a'a ai ba fa wani girma can yayi ba ta fad'i mata watannin shi Aunty tace to amman dai gaskiya in haka ne zata yi girman ciki yadda cikin farko bai cika wani girma ba k'ilan dai da gaske yan biyun ne, ita dai murmushi kawae take yi, bayan ta aje Hijab d'in ta nufi gadon ta haye idon ta akan Aunty Mareeya tace "kiyi hak'uri jiya kinata jira na naga dare yayi shine na yanke bari sai yau in zo in fad'i maki komai baki da baki" da sauri tace ai ba komai dama itama bata san ran a jiya zata kira ta fad'i mata yadda sukai ba ba kamar data ce bai gari,
"Na tambaye shi duk abunda kika ce harma da wanda baki ce ba wato aikin shi" a k'agauce Aunty tace aikuwa fa ba'a san aikin shi bama wllh to yanzu ya sukai da shi, tiryan tiryan ta shiga yi mata bayanin duk yadda sukai da Haisam gaba d'aya sun maida hankalin su akanta harda Fauzyn tayi cak tana kallon bakin Fatun, tun kafin ta rufe baki Aunty ta shiga washe baki ta fara fad'in "Alhamdulillah, Alhamdulillah dama ni wllh ban ji ina zargin shi da komai ba kawai a rai na ina jin sakayya ce ubangiji zai mata da shi" Murmushi Fauzy kawai ke saki bata ce komai ba Aunty ta kalle ta tace "to kin ji dai ai yanzu sai ki kwantar da hankalin ki tunda ga bayani nan daga bakin mai dil gashi nan kuma da kan shi yace abun kiyi Alfahari ne ma ita matsalar tashi da aka ce kada ki d'auketa a babbar matsala ke zaki zage damtse ki hana shi hakan sannan ki kore mayun kudajen matan da ke bibiyar shi wannan duk mai yuwuwa ne ba kamar in kika shige daga ciki in sha Allah za muyi k'ok'ari ya dawo bai sha'awar ta6a kowacce mace in ba ke ba" murmushi kawai Fauzy ke saki haka ma Aunty Mareeyar sai faman washe baki take gaba d'aya dad'i ya cikata farinciki ne bayyane akan fuskar ta can tace ma Fatuu to miye aikin shi data tambaya bata fad'i masu ba,
bayanin aikin nashi ta shiga yi tun kafin ta gama yanayin fuskar Aunty ya fara sauyawa lokacin data gama fad'i masu gaba d'ayan su zaro ido sukai da alamun razana Aunty tace wai bata gane su ke yin rocket ba wai wadda ta sani ko kuwa, Fatuu na dariya tace mata eh, aikuwa gaba d'aya ta k'arasa zaro idanun ta kai duka hannuwanta ta dafe k'irji tace "na shiga ukku ni Mariyatu, Zarah wannan abun fa ba shine ake ce ma makamin k'are dangi ba yanzu ace su suke yin shi" sosae ta rud'e don yanayin fuskar ta ya bayyana still dariya Fatuu ke yi tace mata itama wllh farko saida hankalinta ya tashi amman ai yace shi yafi k'arfi ta bangaren had'a jirgi kuma ba kowanne rocket ne missile ba, yarfa hannu Aunty tay ta d'an cize baki tace "ki gane Zarah irin abun nan ko wanda yasan inda ake saida su dole kaji tsoron shi balle kuma wanda ya san inda ake k'era su yake kuma aiki a wurin, haba, haba kice dole ma Sameer yak'i dariya suda ke k'era wannan mugun abun tashin hankalin ta ya zai rink'a ma sakin fuska, ai wllh Fauziyya ko baki son shi yanzu yazama dole ma ne ki amince mashi in dai ba so kike ya k'arar da kaf dangin mu ba koma ya tashi garin Funtua gaba d'aya",
Fatuu mi zatayi in ba dariya ba harda dafe ciki da 6ungulawa saman gadon don gaba d'aya Aunty fa ta rud'e, ita kanta Fauzy duk da ta d'an razana amman sosae Aunty ta bata dariya, bayan Fatuu ta tsagaita da yin dariyar ta taso zaune nan ta shiga kwantar ma Aunty da hankali tana nuna mata shifa ba'a ce dashi ake k'era wannan ba kuma koda dashi d'in shidai ai sana'a ce yake kuma misali don suna k'erawa hakan ba yana nufin sun iya amfani da shi ba tunda hakan ma wani ilimin ne, fuska a kwa6e Aunty ke kallonta hakan ya k'ara ba Fatuu dariya, da k'yar dai aka samu Aunty ta d'an kwantar da hankalinta Fauzy ta zuba mata alkubus ta fara ci duk in Fatuu ta kalleta sai ta saki dariya ita kuma saidai ta d'an girgiza kai ta tura Alkubus a baki, itama ta yaba alkubus d'in tana cikin ci tace ma Fauzy sai ta tsaya ta koya Abinci sosae in ba haka ba taje ta kwa6a mashi ya tarwatsa ta da rocket ita ta sani gaba d'aya suka kwashe da dariya Fauzy na fad'in ai fa sun bani da zancen rocket, bayan ta gama ci Fauzy tace yanzu sai ta kira Baban ta sanar mashi ko tana harararta tace ta sanar mashi da uban mi da ba tace bata son shi ba, Fauzy na murmushi tace to yanzu tana son shi Saboda kar a tashi Funtua suka saka dariya harda ita Auntyn,
Kiran Mahaifin nasu ta shiga yi tana fara ringing ya d'aga cikin girmamawa ta gaishe dashi tare da tambayar yadda suke duk ya amsa mata, a nutse ta shiga yi mashi bayanin sun yi magana da Fauziyya kuma ta nuna tana son shi har ma sun yi bincike akan shi, nan ta kwashe komai ta sanar mashi amman banda zancen ta6a mata da aka ce yana yi, nannauyar ajiyar zuciya mahaifin nasu ya saki yay d'an jimm har saida Aunty ta tambayi Lafiya da yanayin damuwa a muryar shi yace to ai abun ne ba K'aramin Al'amari bane d'an Governor fa, Aunty tace "Don Allah kar ka wani tashi hankalin ka Baba ai Allah baya daurawa bawa abunda bazai iya ba, kuma ai shi yaron yasan ita wacece tunda ta sanar dashi har ma aiki daka ajiye da noma da kake yi yanzu duk ta sanar mashi tunda yaji ya gani to kaga ai ba abun damuwa bane kuma dama ai ance wani hanin ga Allah baiwa ne k'ilan sakayyar abunda Mujaheed yayi mata ne" jinjina kai yay ya furta hakane kafin yace yanzu ita ya take ganin za'ayi don shi wllh gaba d'aya kan shi ya d'aure ganin abun yake ma kamar wani al'mara, dariya tayi tace ba al'mara bane da gaske ne ta kuma cewa "abunda nike gani Baba shine ka kira su kamar yadda kace masu sai kace cikin weekend mai zuwa in yayi masu sai su zo" shiru yay kafin yace mata hakan bai yi kusa ba kuwa tace a'a ai tunda neman Aure ne za'a zo ba wai bikin ba gara kawai a basu dama yanzu zata yi ma Yaya Mubarak magana duk abunda ya dace za'a yi in sha Allahu itama in dai zasu zo lokacin tana tunanin zata zo, a sanyaye yace Shikenan zai kira su d'in duk kuma yadda sukai zai kira ya sanar mata tace to, fatan Alkhairi yayi ya saka masu Albarka daga haka sukai sallama, suna gamawa ta k'ara ma wayar kud'i ta bank ta kira Mahaifiyar su, kamar yadda sukai da Baban nasu haka itama tayi mata bayani, sosae itama jikinta yay sanyi daga yanayin muryarta tace mata yanzu ita tana ganin hakan mai yuwuwa ne Aunty tace in sha Allahu su yi Addu'a kawai tace Shikenan zasu yi, bayan sun gama wayar kallon Fauzy tay da tay zuru ita kanta na Baban nasu ganin abun take kamar al'mara d'in tana murmushi tace mata to ta kira Baban nasu Fauzyn ta d'an ta6e baki tace umm Fatuu ta kai hannu ta dafata da murmushi tace wannan ba abun damuwa bane abun farinciki ne k'awata tay yar dariya,
"Yanzu ni abunda nike gani in sun amince zasu zo Weekend d'in kar a wani ce za'a takura kai tunda nasan maza ne masu zuwa kuma ko gidan namu suka gani zasu fahimci irin k'arfin mu, yanzu bari in je d'aki in natsu sai in kira Yaya Mubarak d'in tunda shine mai kud'in gidan yana aiki kuma dama ko ba yanzu ba kullum cikin yin hidima yake sai mu tsara abunda ya kamata duk dai a taru a had'a k'arfi da karfe, ina ganin har fenti yakamata ayi ma gidan sannan tunda a parlon Baba za'a tarbe su sai a gyara shi sosae a canza kujerun ciki da duk abunda yakamata, gaskiya dole ma in je" ta k'arasa Maganar tana jinjina kai, a sanyaye Fauzy tace to banda gadon Baban za'a canza Aunty tace tana tunanin ba sai an canza dashi ba tunda a parlor ai za'a zauna,
"Amman in suka ce zasu kwana fa?" Fauzy ta fad'a fuska a d'an yamutse, shiru Aunty tayi alamar nazari can tace gaskiya bata tunanin hakan su fa manyan mutane basu kwana wuri irin haka in ma ta kama masu a Hotel suke sauka amman ko don k'ilan su buk'aci shiga yin alwala ko wani abu akwae buk'atar a canza d'in hatta toilet d'in ma a gyara shi abunda ke buk'atar canzawa a canza, kai Fauzy ta jinjina sai kuma tace ma Aunty Mareeyar akwae kud'i a account d'in ta sai a had'a dasu da sauri tace Yauwa to aikuwa zasu taimaka sosae tunda suna da d'an yawa tana rufe baki Fatuu tace itama bari ta tura mata gudunmawarta duk sai a had'a,
"A'a Zarah don Allah ba sai kinyi wata dawainiya ba tunda kema ai baki rasa uzurorin kud'i ko" d'an murmushi tayi tace "ai Aunty Mareeya shine yanzu uzurin ya taso ko, ko bamu zama yan'uwa bane?" da sauri ta girgiza kai "tabbas mun zama Zarah, tun tuni ma" yar dariyar jin dad'i Fauzy tayi, nan take ta turo ma Fauzy 300k lokacin data duba alert d'in gaba d'aya ta zaro ido baki bud'e