Showing 339001 words to 342000 words out of 512766 words
Chapter 114 - Asanadin Makwabtaka Book 3 Hausa Novel Complete
Unknown
27 Dec 2024
1548
and I couldn't remember in akwae wani rana da nayi bakin ciki Saboda ke in ma akwae shi kenan, ban ta6a shiga damuwa ba sosae kaman ranar da zamu rabu zan yi aure, tun lokacin dana fahimci kin canja man na fara shiga damuwa har zuwa ranar, sosae kikai breaking heart d'ina har yanzu ina ganin image d'in wannan moment na ga Zarah a duk'e tana kuka sosae Saboda Ya Handsome d'inta gashi ni kuma ba abunda zan iya yi mata kan hakan, idanuwa na sun cika da tears a lokacin wanda bazan tuna when last naji hakan ba, koda muka shiga jirgi saidai kawae na d'age kai na na runtse ido ba komai nike ba sai tunanin halin dana baro ki a haka har muka isa Abuja...." Murmushi kawai Fatuu ke yi yayin da zuciyarta ta shiga tariyo hoton rabuwar tasu a airport, a lokacin wani irin soyuwa zuciyarta ke yi gaba daya ji tay kaman rayuwarta tazo k'arshe she felt empty, rayuwa kenan yanzu gashi komai ya zamo tarihi a gare ta duk sanadiyyar hak'uri da tawakalli,
"Ranar da kika sanar man zaki abortion naji tashin hankali amman bai kai na ranar da kika fad'i ba a wurin Dinner party, that was the second day dana shiga tsananin tashin hankali a rayuwa ta, daga ranar dana rasa grandpa dina mijin Hajiya lokacin ina a Secondary school sai kuma wannan ranar ganin Zarah kwance a jikina bata numfashi , zuciyata tayi ta sak'a man abubuwa....." Labarin irin halin daya shiga lokacin da zasu kaita Asibiti harda kukan daya yi ya shiga bata yana ta murmushi har ya gama ta hau girgiza kai har saida taji idanunta sun ciko da k'walla wata irin k'aunar shi take ji na ratsa mata jinin jikinta, Sigh yay ya kalleta da murmushi yace daga bayanin aikin shi da yayi mata ta fahimci abunda take son sani na wanda yafi samun kud'i tsakanin shi da Sameer, yamutsa fuska ta shiga yi a shagwabe tace itafa wllh hakanan ta tambaya ba don wani abu ba kawae subul da baka ne,
"ai dama kin cancanci kisan komai game da aikin mijin ki ko" ya fad'a yana murmushi, d'age mashi gira tay tace "to in haka ne ka fad'i man nawa ne salary en ka" tana rufe baki yay mata wani kallo mai kaman harara ta saka dariya tace to ba shi yace ta cancanci tasan komai ba,
"Wannan sirri ne banda shi" ya fad'a yana yar dariya itama har lokacin Dariyar take tace mashi ita bata yarda ba sai ya fad'i mata ai shi yace, ce mata yay to zai fad'i mata amman a kunne zai rad'a mata don kar aji, har saida ta d'an Jujjuya kafin ta tsaida idonta akan shi tace to ba su kad'ai bane, hannu ya mik'a ya nuna mata cikinta yace Baby yake nufi kada ya fad'a mata ya ji wata rana in ya buk'aci ya siyo mashi/mata abu yace baida kud'i ace mashi yana dasu tunda an ji salary d'in shi daya fad'i ma Mom, dariya sosae Fatuu ke 6a66akawa tace to ita bai gudun tayi mashi hakan sai Baby yace ai ita ya gane tausayinshi take ji bata son yana kashe kud'i amman yasan k'ilan in ya fad'i mata ta daina jin tausayin nashi da sauri ta d'aga hannu tace to Allah bata son jin salary d'in tay Maganar tana dariya tare da girgiza kai shima still dariyar yake, bayan sun tsagaita gaba d'aya jingina sukai da jikin kujerar suna kallon juna kowannansu wani irin nishadi yake ji duk ya kasance da d'an uwan shi,
"Na dawo daga tafiya kin hana ni in huta da tambayoyin ki" ya fad'a bayan yayi yar hamma, jin haka yasa ta sauke k'afafunta daga saman jikinshi da sauri ta fara k'ok'arin mik'ewa tana fad'in yayi hak'uri to ya tashi suje su kwanta, nuna mata bowl data sha fruit salad yay yace ta kai Kitchen bari ya kashe kayan kallon tace to, lokacin data dawo cikin parlon har ya kashe kayan kallon yana ganinta ya mik'e tsaye ta nufo shi tana murmushi, tana zuwa gaban shi kawae sai ta juya mashi bayan ta d'an rankwafa tace wai ya hau ta goya shi tunda shi bai iya goya ta Saboda ciki, dariya sosae ta bashi aikuwa tana a yadda take taji ya sunkuce ta gaba d'aya ta saka dariya, nufar hanyar Bedroom yay yana d'auke da ita ta sak'alo hannuwanta a wuyan shi tace wai bai jin nauyinta Slowly ya furta ai dama gaba d'ayan su nauyin su na a kan shi don haka bai jin shi, suna zuwa bakin kopar d'akin yasa k'afa ya tura ya shige da ita.........
_Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wad'annan nos din 09013804524 ko 08169856268
91
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
............Washe gari Asabar Misalin k'arfe sha d'aya na safe Mom na kwance ta koma bacci bayan sun yi Breakfast, tana cikin baccin ta jiyo ringing d'in wayarta kamar bazata tashi ba da k'yar dai ta bud'e idanun ta ta kai hannu gabanta ta d'aukko wayar, duba screen d'in tay taga wanda ya kira har saida tay d'an yi murmushi ganin yar uwarta ce wato Hajiya Zainab, picking tay ta kara wayar a kunne, gaisawa sukai da juna jin yanayin muryar Mom d'in yasa tace yar gayu bacci ma take ko ta tasheta, Mom na murmushi tace gayu ai sai ita kawai ta koma bacci ne Hajiya Zainab na murmushi tace to ai saida hutu ake iya komawa baccin,
"Hhhh in wannan hutun ne ai kowa ma nada shi kema nasan baki so kwanciyar bane",
"Uhmm wani lokacin kam ai ko kaso ba dama ka koma Saboda schedules" Mom na murmushi tace ya za'ai sai Addu'a Allah ya k'ara d'aukaka ya kuma taimaka tace Amin,
"Sai kika ji Saraki ya samu Mata" shiru Mom tayi tana maimaita sunan Saraki da ta fad'a, da alamun rashin fahimta tace "mi kike son fad'i man, ba dai his Excellency ne zai aure ba?" Dariya Hajiya Zainab ta saki tace "inaaa, ai Excellency ya gama yin aure a gidan duniyar nan ya auru yadda ya kamata, Saraki wanda yay gadon Sarautar Grandpa nike nufi" shiru tay tana nazarin Maganar da tayi can tace "wai Son kike nufi?"
"Eh mana, wai kina nufin baki sani ba duk da anan gidan ya samu Matar" kan Mom ne ya d'aure ba shiri ta yunk'ura ta tashi zaune jikinta sanye da kayan bacci, ce mata tayi ita bata san da wannan Maganar ba gaskiya amman wacece wadda zai auran, fad'i mata game da Fauzy ta shiga yi, sosae Mom taji mamakin Maganar har tama kasa magana saida ta nisa sannan tace,
"Amman dai abun da mamaki wllh ace Saleem da kanshi yace yana son Auren yarinyar" daga d'aya bangaren Hajiya zainab tace "Wllh, it was a real surprise, kinsan farko Dad d'in shi ya tunkara da Maganar wai ya samu wadda zai aura ya tambaye shi a ina nan yake ce mashi yar Funtua ce tana karatu a Katsina koda Dad d'in nashi ya tambaye shi d'iyar waye sai cewa yay shima bai san shi ba kawai dae yasan Dad d'inta is a retired man yanzu Farmer ne, sosae shi kan shi Dad d'in nashi yay mamakin jin yarinyar da yake so ya Auran daga baya ya tuntu6e ni da Maganar ya tambayi wai ko nasan ta nace bazan iya tuna ta ba koda na ganta da bikin, amman I never thought Sameer would fall in love with such a local girl wllh, nayi mamaki ba kad'an ba duba da irin matan da ake mashi tayin auren su, kinsan ko bayan bikin Son saida muka shirya mashi had'uwa da yarinyar sarkin zazzau wadda Mom d'in ta Friend d'ina ce baki gan yarinyar ba very beautiful girl wllh gashi Kusan complexion d'inta iri d'aya da Sameer d'in don Mom d'inta balarabiyar Sudan ce bata dad'e da dawowa daga Saudiyya karatu ba shine Mom d'in nata tayi man Maganar mu gwada had'a su don tana son Sameer sosae, wllh Sis in gaya maki nasa yarinyar tazo nan ta kwana biyu wai don in yi kokarin had'a su, ranar dana kira shi don su gaisa a parlor ko kallon direction d'in da take bai yi ba saida nayi introducing nata sannan ya d'an kalleta daga baya nace bari in basu wuri su san juna sosae, na d'an jima sannan na koma parlon kawai sai na ganta zaune ita d'aya da mamaki na tambayi ina yake tace man ai ina tashi shima ya bar wurin baki ji yadda naji ba kunyar yarinyar ya kamani....."
Murmushi Mom tayi ta d'an girgiza kai,
"........Lokacin na iske shi a d'aki nace mashi miyasa zai baro falo bayan na tashi da bud'ar bakin shi sai cewa yay dama ba gaisawa ne zasu ba kuma sun yi hakan, sototo nayi ina kallon shi don na tabbatar ya san mi hakan dana yi ke nufi don ba yau ne na farko ai da aka had'a shi su gaisa da mace ba an yi hakan sau da dama kama daga yaran k'awayena dana Abokan Dad d'inshi har fa akwae d'iyar shugaban wurin aikin shi baturiya da shima shugaban nasu yaso had'a su amman yak'i har nan Nigeria ta ta6a biyo shi itama kyakkyawa duk da ba musulma bace, koda na nuna mashi ina son ya auri ita Raudha d'in data zo sai ce man yay bata yi mashi ba yarinyar da ko kallon Arziki bai mata ba taya zai san tayi mashi, lokacin na nuna mashi 6acin rai na kan to har sai yaushe ne zai samu wadda zata mashi yay aure kawai sai ya yi man wannan shu'umin murmushin nashi yace wai in kwantar da hankali na ya samu Mata soon zai yi aure, wllh ni duk na d'auka ya fad'a ne kawai Saboda in bar zancen Rauda ashe da gaske ne yarinyar nan yake nufi",
nannauyar ajiyar zuciya Mom ta sauke ta furta "ina ruwan Son amman dai wllh it was a real surprise to hear that Sameer has chosen that girl to be his wife, duk da dai gaskiya yarinyar ba mummuna bace tana da kyaunta daidai gwargwado amman dai dole ai mamakin jin ita ya fitar a matsayin mata kinga kaman shi Habiby ba za'ai mamaki ba sosae da yarinyar da ya aura tunda ba itace ta farko ba",
"Uhmm, ni kinga ma na kasa gane yarinyar yace man wai best friend d'in ita matar Son ce"
"Eh hakane, amman zaki iya tuna wata yarinya da aka kira ta bada biography na ita Amaryar a wurin dinner? Kaman itace mace ta farko data yi magana a wurin" shiru Hajiya Zainab tayi da alama tana k'ok'arin tunanowa ne can tay d'an tsoki tace bata jin zata tunata Mom tace bari ta duba cikin pictures d'in bikin tasan akwae hotunan ta sai ta turo mata ta gani tace Ok,
"To yanzu ya za'ai kenan? zaku amince mashi ya aure ta ne ko kuwa a'a" yar ajiyar zuciya Hajiya Zainab tayi tace "to, tunda yaji ya gani ita yake so ai Shikenan tunda bamu zamu zauna mashi da ita ba abu har ma an kira Mahaifin yarinyar kan Maganar, saidai bazan 6oye maki ba sam hakan bai kwanta man ba ba kuma don wani abu ba wai game da yarinyar kawai dai akwae wad'anda naso ya aura sosae kinga har Daughter Jahad nayi k'ok'arin had'a su saidai ban matsa mashi ba daya nuna bai so Saboda dama nayi tunanin ba lalle tayi mashi ba zai iya ganin tayi mashi k'arama to k'arshe gashi nan k'aramar ya samo zai aura" wata ajiyar zuciyar Mom ta k'ara yi cikin kwantar da murya tace "in dama Allah ya k'addaro ita ce matar tashi no matter what sai ya auretan don haka muyi mashi fatan Alkhairi kawai don kinsan in namiji na son Mace idon shi makancewa yake yanzu ga dai Son nan na fahimci ba K'aramin son Amaryar nan tashi yake ba" murmushi Hajiya Zainab tayi ta tambayi ya jikinta Mom d'in tace lafiya lou take ko laulayi bata yi tun kafin ma ta bar Abuja cikin har ya fito Hajiya Zainab d'in tace Allah sarki tayi fatan Allah ya sauketa lafiya Mom ta amsa da Amin,
"Jiya mun yi waya da Ummi da Abie" Hajiya Zainab ta fad'a Mom tace "eh haka suka ce man da na kira su da daddare, wai don Allah bazaki mana k'ok'ari ba su dawo nan kusa damu kamar yadda mukai magana kwanaki" dariya Hajiya Zainab tayi tace "ai tunda nayi ma Ya Othman magana kan hakan yace muma fidda rai bazasu ta6a dawowa Nigeria ba na hakura, kuma suma basu so" Mom na dariya tace "ban ga laifin su ba wa zai so ya baro k'asa irin Qatar ya dawo Nigeria dama dai a Ethiopia suke ne"
"Wllh, ai Al'amarin K'asar nan sai Addu'a kawae amman tak'i cigaba har yanzu baya muke sosae a abubuwan cigaba da dama" Mom tace "uhmm ai kune zaku taimaka mana ku farfad'o mana da ita" tana jiyo sautin dariyarta tace su a suwa suda suke k'ananu Mom tace to Allah ya dubesu ya kawo masu Shuwagabannin da zasu kawo cigaba ta amsa da Amin daga baya suka cigaba da Magana dangane da neman Auren Sameer,
Misalin k'arfe ukku Fatuu ta fito daga wanka tana zaune a gaban mirror tana shiryawa yayin da Haisam ke kwance a gado yana baccin rana, shirin zuwa gidan su Fauzy take kamar yadda ta yanke zuwa yau tayi masu bayanin da Haisam yayi mata game da Sameer, bayan ta gama yin shafa ta mik'e ta nufi Wardrobe, doguwar bak'ar riga roba ta fiddo ta saka rigar d'an guntun hannu gareta ta bi jikinta cikinta ya fito sosae bayan ta gama sakata ta kai hannu ta fiddo wani lifaya lace bak'i mai adon fulawowi ja da silver, musamman dama taje Hajiya ta koya mata nad'a lifaya kwanaki Saboda tana dasu a kayanta, gaba d'aya sark'a da yan kunne silver ta saka masu kyau sai Agogo shima silver, gaban mirror ta dawo tayi d'aurin kallabi Zarah buhari da wani bakin kallabi, sosae shigar tayi mata kyau sai faman sakin murmushi take, takalma Flat ta d'aukko silver sai yar purse, gado ta nufa bayan ta gama ta zauna ta bangaren da Haisam yake tana kallon yadda yake baccin hankalin shi kwance, murmushi ta shiga saki ta matsa saitin fuskar shi ta rankwafa tay pecking kumatun shi, tana d'agowa ya bud'e idanun shi slowly suka shiga cikin nata, bin ta da kallo yay kafin a hankali taji ya furta "kin yi kyau sosae" murmura mashi ido tay tace ta gode,
"Na gama shiryawa zan tafi" kai ya jinjina yace Ok bari ya kaita, da sauri tasa duka hannuwan ta akan shi alamar kada ya tashi tace ita zata je da kan ta, d'an waro ido yay cikin murya ta wanda ya tashi daga bacci yace "hannun ki fa bai fad'a sosae ba...." Da sauri ta katse shi "Wllh kau lafiya lou yanzu na iya driving d'in sosae rannan ma ba ni na kai mu School ni da Mino ba, wani kallo yay mata "amman ai ina Motan ko" tura mashi baki tay ta fara shagwa6a tana fad'in Allah lafiya lou zata je ai tana fita ita kad'ai taje gidan gwaggo ko, shiru yay kawai yana kallonta tace to bari taje sai yazo ya dawo da ita, kaman bazai ce komai ba sai kuma taga ya lumshe mata ido ta washe baki ya furta "You should be very careful pls" da sauri ta jinjina mashi kai, saida ta k'ara pecking lips d'inshi sannan ta mik'e yace bari yazo yaga fitar ta tace a'a don Allah yayi baccin shi, girgiza mata kai yay ya yunk'ura ya tashi zaune, yana ruk'e da hannunta suka fito daga cikin d'akin tace bari ta d'aukko abu a kitchen, bada Jimawa ba ta fito ruk'e da madaidaicin basket mai kyau acikin shi luxury Warmers ne guda biyu Abincin rana da tayi ne dama ta zuba zata kai ma su Fauzy,
Bayan sun iso parking space d'in shi ya shiga ya fiddo mata da Motar cikin harabar, bud'e kopar driver seat d'in yay ba tare daya fito ba yace mata ta bari suje kawai ta nok'e mashi kai tana d'an yamutsa fuska tace to in ba'a bari tana fita ita kad'ai ya za'ai ta saba, shiru ya d'anyi yana kallon ta har lokacin idanun shi a d'an lumshe suke, ba yadda ya iya tunda ta nuna tana so ya fito ita kuma ta shiga ta zauna sai faman sakin murmushi take bayan ta daidaita natsuwar ta ya rufe mata kopar, sauke glass tayi ta kashe mashi ido tare da furta kada ya damu ai yasan matar shi nada saurin gane abu yay murmushi kawai tace ya shigo ta aje shi a bakin gate sai ya koma ya girgiza kai yace zai koma, yana tsaye taja Motar ta tunkari gate Officer ya taso ya zuge mata shi da zata fita ya d'aga mata hannu tare da Fad'in Allah ya tsare ta sakar mashi horn, Jama'a kuzo kuga Fatuu yar fillo na tuk'a Jeep abun na Allah ne, bata yi tunanin tsayawa ba a gidan su shagon Kawu Amadu ma a rufe yake tasan bai wuce yana ciki yana bacci ta wuce.
Alhamdulillah, lafiya lou ta k'araso kopar gidan su Fauzyn, bayan ta parker ta fito kopar baya ta bud'e ta d'aukko basket d'in Abincin bayan ta rufe Motar tana niyyar nufar cikin gidan wayarta ta fara ringing tun bata ga mai kiran ba ta gane Haisam ne, d'auka tayi tana yar dariya tace ya kwantar da hankalin shi gata ta iso lafiya a hankali ya furta Alhamdulillah, tambayar shi tayi halan ma bai koma baccin ba yace mata ya kasa Saboda tunanin ta tane dariya tace to ai yanzu sai ya koma kafin ai la'asar ya furta Ok,