Showing 348001 words to 351000 words out of 512766 words

Chapter 117 - Asanadin Makwabtaka Book 3 Hausa Novel Complete

Unknown   

27 Dec 2024

1605

da fad'in "Yauwa Aunty nima wllh ina tunanin haka, amman tunda ga bikin Mino za'ayi mi zai hana muyi kokari muyi masu wani abu da zasu ji dad'i sosae" kai Aunty ta jinjina "tabbas kuwa kin kawo shawara duk da bansan a cikin ku bikin wa za'a fara yi ba amman koma dai nawa aka fara ba abunda zai gagara kinga in ma naki aka fara komai zai zo mana da Sauk'i don lokacin nasan Atm Card d'in Sameer ya riga ya dawo hannun ki" Dariya sosae Fauzy ta saka tana fad'in kai aunty kin jiki da wata magana, bayan sun gama tattaunawa sukai ma juna sai da safe, a ranar kowa kwanan farinciki yay tsakanin Aunty da Fauzy da kuma Fatuu.

A kwana a tashi ba wuya a wurin Allah, ranar Alhamis tunda safe Aunty ta tafi Funtua, zuwa karfe sha d'aya ta isa gida lokacin data je har anyi ma gidan Fenti mai kyau kamar yadda sukai da Yaya Mubarak d'in su gaba d'aya gidan ya haske layin nasu dama kuma yana d'aya daga cikin gidaje masu d'an kyau a layin nasu, bayan sallar Azahar suka tafi inda za'a siyo furniture da ita da Kishiyar Maman su wadda itama suka d'auketa tamkar uwa a gare su don sam basu taso suka ga suna kishi ba da Mahaifiyarsu in ma suna yi to ba irin na tada fitina ko munafunci ba, wasu daga cikin K'annansu ma sai da suka girma ne suke gane wacece maman su, da yake Funtua akwae wuraren saida had'addun furniture da dama basu wani sha wahalar za6ar inda zasu ba don sun san inda zasu samu irin wanda suke so, bayan sun je wurin wanda katafaren bene ne sama da kasa duk kayan katakon ne iri daban daban, Manager d'in wurin suka buk'aci gani bayan anyi masu jagora wurin shi suka gaisa sannan Ya Mubarak yayi mashi bayanin dama kakara suke son suyi akwae kaya da zasu siya su kuma zasu za6i wasu sai suyi ciko cikin faran faran yace wannan ba matsala bane tunda suna yin hakan ya buk'aci ganin kayan suka sanar dashi suna gida amman akwai hoton su a waya, nuna mashi Vedio d'in kayan mahaifin nasu sukai ya gani kafin yace akwae buk'atar ya tura aje a gansu sai ayi masu kud'i sannan ayi cininkin, Yaya Mubarak ne yace to ba matsala a had'a shi da wanda zasu je d'in sai suje su dawo, ba 6ata lokaci aka had'a shi da Mutum biyu da zasu tafi Aunty Mareeya tace don Allah su kamanta ayi siyan mutunci Manager da suka fito tare da shi cikin show room d'in yana dariya yace karta damu su suna kamantawa sosae, a nan Aunty da Kishiyar Maman tasu da suke kira da gwaggo suka zauna akan kujeru don su jira su. Basu dad'e can sosae ba suka dawo ba laifi kam sun sayi kayan da mutunci don d'aki barin katako ne ba don dole tasa ba daba yadda za'ai Baban nasu ya yarda su siyar mashi da kaya Saboda yana son su ba tun yanzu bama sun so canza mashi kujerun yak'i yarda, za6ar wanda suke so suka shiga yi nan fa suka shiga ruwan idon wanda ya kamata, Manager d'in wurin ne ya basu shawarar d'aukar wasu lumbutsa lumbutsan leather chair yace tunda yaji suna d'akin mahaifin su zasu saka tunda shi Namiji ba'a san shi da k'yale k'yale ba, sosae kujerun sukai masu kyau saidai Aunty Mareeya tace ita abunda ke had'a ta dasu 6an6ara suke Manager yace ba dai irin wannan ba ai ko ita ta kalli leather d'in zata shaida ingancin ta yana mai tabbatar mata da ba abunda suke yi don ko shi irin su ne a parlon shi Aunty na dariya tace kodai abun su na yan kasuwa zai masu yace in yayi haka kuma ai kan shi ya kashe ma kasuwa ko, k'arshe dai su suka za6a harda dining table d'in su mai kujeru shidda, bayan sun gama da nan sama suka hau inda gadaje suke basu wani yi ruwan ido anan ba don sun san wanda ya dace su d'aukar mashi, bayan duk sun gama za6a Manager yace masu harda d'inkakkun labulaye suna dasu da agogunan bango in suna so Aunty tace yauwa bari su duba ya jagorance su nan ma suka za6a, bayan duk sun za6i abubuwan da suke so aka buga lissafi suka yi ciko wanda ya lillinka kud'in da aka Siya kayan nasu sosae, dama shima Ya Mubarak d'in ya bada tashi gudunmawar haka Baban su ma da yake ba K'aramin samu yake da Noma ba Saboda tsohon ma'aikacin Ktarda ne kuma ya kai babban matsayi kafin ya aje aikin banda babbar gonar da yake da ita anan garin yana da wasu k'ananu zasu kai ukku a wasu kauyuka dake kewaye da garin da alama dai Fauzy harda rud'ewa tasa tace ma Sameer mahaifin nasu bai iya biyan shi wayar data fasa mashi, a babbar Motar kamfanin aka zuba kayan su Aunty na gaba a Motar Yaya Mubarak suka tafi, bayan sun isa gidan tuni k'annansu har sun fito dana mahaifin nasu ta kopar shiga sitting room d'in shi ta waje, nan fa aka shiga sauke sabbin kayan yan unguwa suka shiga baza ido suna kallo, bayan angama aka d'aura nashi yan kamfanin suka tafi. Aiki ga mai k'are ka, aifa Aunty Mareeya bata ga ta zama ba dama ita ba mai son jiki bace bare abu kuma irin wannan nan fa suka zage ita da k'annanta maza da mata harda masu Aure guda biyu da suka zo aka shiga shirya parlon dama kuma tiles ne a k'asan kuma sam bai ji jiki ba Saboda ba yawan zirga zirga ake part d'in ba, zuwa bayan sallar La'asar sun gama komai gaba d'aya sashen ya koma kamar na Amarya sosae yay kyau yan gidan sai faman washe baki suke ba kamar yara sai tsallen murna suke, Vedio Aunty tayi ta tura ma Fauzy daga baya ta kirata ta sanar mata ta hau online ta gani, lokacin data yi arba da vedion bud'e baki tay ta waro ido nan ta shiga washe baki tana yarfa hannu sai faman fad'in Wayyo Allah take, da yamma mai gyaran Ac yazo don tuni ta lalace bata yi haka mai gyaran toilet ma, yan unguwa fa kan su ya kulle wasu da basu iya hak'uri sai tambayar ko biki ake gidan saidai ace masu a'a don Mahaifin nasu ya gargad'esu kan su ja baki suyi shiru sai komai ya tabbata. Sai da daddare Mahaifin su ya dawo gidan nan gaba d'aya aka taru a sashen nashi sai farinciki ake shima dai fuskar shi ta kasa daina murmushi Yay Addu'ar Allah ya tabbatar da Alkhairi duk suka amsa daga baya aka watse. Washe gari Friday shirye shiryen Abincin tarbar bak'i aka shiga yi da wuri su Aunty suka shiga kasuwa, a gidan Yaya Mubarak aka shirya za'a yi komai harda Warmers d'in da za'ayi amfani dasu plate duk anan za'a k'aro don Aunty Mareeya ta taho da wasu jigunannun Warmers d'inta dasu plates da sauran su.

Alhamdulillah Allah yayi dare gari ya waye an shigo Asabar lafiya, tun da sassafe yan gidan suka tashi aka hau gyaran gida masu aikin Abinci duk acan gidan Yaya Mubarak d'in suka kwana, Misalin k'arfe sha biyu na rana bak'in suka iso garin, kiran Mahaifin su Fauzy sukai suka sanar dashi game da isowar tasu don aje ayo masu jagora, dama Yaya Mubarak na gidan isowar su kawai ake jira shi ya tafi don ya taho da su, bada jimawa ba suka iso layin gidan Motoci guda biyu ne d'aya jibgegiyar bakar Jeep ce wadda anan bakin suke sai k'arama wadda itama bak'a ce sai faman salk'i motocin suke anan kuma security ne cikinta gaba da baya don a cikin bak'in harda Commissioner wanda d'an uwa ne kuma abokin mahaifin Sameer d'in ne sai sauran mutum biyun d'aya k'anin Governor d'in ne uwa d'aya uba d'aya sai d'ayan cousin brother d'in Governor d'in ne matsayin Yayan shi yake, Mahaifin su Fauzy ne tare da yanuwan shi guda biyu sai Yaya Mubarak da wasu daga cikin manyan Yayan shi maza guda ukku suka tarbe su cikin girmamawa kowanne cikin bak'in na sanye da babbar riga ta alfarma mutum biyu farar shadda ce sai d'aya ash, security d'in wanda jami'an yan sanda ne guda biyu sai guda biyu na civil defence ne su basu shiga ba suna a cikin Motar amman sun bud'e kopopin sai lokacin Jama'a suka samu abun baza ido da kyau yara da Almajirai ba sosae ba duk sun tsaya cirko cirko suna kallon Motocin haka Mutanen dake wucewa kowa idon shi na akan Motocin da kuma wad'anda ke zaune a bakin shaguna sai faman tambayar juna abunda ke faruwa a gidan suke wanda kuma ba mai amsa. A mutunce aka shiga gaggaisawa parlon sai zabga uban k'amshi yake daga baya aka fara gabatar da kai, su Aunty Mareeya ne suka fara shigowa da kayan abinci suna jerawa a saman Dining duk sun yi wanka sun sa kaya masu kyau, bayan sun gama suka shigo parlon duk suka zauna a saman Carpet suna masu sannu da zuwa tare da gaishe su, haka akai ta shigowa gaishe dasu ana fita, k'anin Governor d'inne da fara'a ya tambayi harda Amaryar acikin wad'anda suka zo gaishe dasu Yaya Mubarak yace a'a ita tana Katsina acan take zaune a wurin Yayarta yayi masu kwatancen Aunty Mareeya suka ce sun gane yace to a wurinta take, bayan an gama yan gaishe gaishen Yaya Mubarak yayi masu Maganar Abinci suka ce da su fara abunda ya kawo su tukun don ba dad'ewa zasu yi ba, neman Auren Fauzy sukai aka basu sannan aka fara maganar saka rana, a yadda suka ce shi Angon so yake asa lokacin da zata gama karatu amman in hakan bai masu ba suna da damar saka duk lokacin da yayi masu, shawara suka shiga yi Yaya Mubarak ne yace yana ganin su shiga ciki sai a tattauna harda iyayen su mata duk suka amince da hakan, ce masu suka yi bari su basu wuri su ci Abinci bayan sun gama sai a k'arasa saka ranar bak'in suka ce to ba matsala duk suka mik'e suka nufi cikin gidan Yaya Mubarak ne ya tsaya don yayi serving nasu Abincin,

A can cikin gidan gaba d'aya sun taru a parlon Mahaifiyar Fauzy harda Aunty Mareeya anata shawarwarin kan lokacin da za'a saka, shi mahaifin Fauzy nuna masu yake gaskiya wata bakwae kamar yayi kusa don yanzu lokaci gudu yake kaman gobe ne za'a ga yayi azo kuma ba'a gama shiryawa ba,

"Ni a ganina Baba kawai a amince da lokacin da Sameer d'in ke so Maganar shiryawa kuma in sha Allahu ba abunda zai gagara watak'il ma fa suce basu son ayi mata kayan d'aki" Aunty ta fad'a,
Malam Sama'ila k'anin Baban nasu ne yace "nima abunda nike tunani kenan tunda dai ai sun fi k'arfin duk wani abu da za'a yi ma Yarinyar",

gwaggo ce tace "hakane, amman dai bai kamata a dogara da hakan ba in dai basu suka ce kar ayin ba yakamata ayi mata komai daidai bakin gwargwado" Baban su ne ya kalli Mahaifiyar tasu yace ita bata ce komai ba tay dan murmushi a sanyaye tace "to ita a ganinta kawai a bi yadda yaron ke so don ko ya aka sa dai lokacin zuwa zai yi kuma indai a cikin wata bakwae ba'ayi shirin daya kamata ba to ko an wuce hakan ba lalle ayi yadda ya kamatan ba" Aunty Mareeya da Baba Sama'ila ne suka ce wannan gaskiya ne, suna haka Yaya Mubarak ya shigo ya gama zuzzuba masu Abincin, bayan ya zauna ya tambayi a wace matsaya aka tsaya Aunty tayi mashi bayani, to shima dai bayan Mahaifiyar su ya bi yace abunda ta fad'a gaskiya ne kawai a amince da hakan ayi fatan Allah ya kaimu ya kuma rufa asiri ai duk ba sai an zurfafa ba tunda dai ansan wacece za'a aura duk aka ce gaskiya ne, dariya Baba Rabi'u wanda Yayan mahaifin nasu ne yayi yace Fauziyya ta giggi6o masu aiki har sai anyi meeting sannan za'a saka mata rana duk akayi dariya. Lokacin da suka koma parlon har sun gama cin Abincin sun dawo sun zauna bayan sun zauna cikin girmamawa su Baba Sama'ila suka tambayi sun dai ci sosae ko suda suka yanko hanya suna fara'a suka ce Alhamdulillah sun gode, cigaba da zancen saka ranar sukai suka ce lafiya lou a saka hakan, tambayar Date d'in da zasu gama Makarantar sukai duk basu sani ba Yaya Mubarak ne ya tashi don ya tambayo Aunty Mareeya, itama cewa tayi bata sani ba aka kirawo Fauzy a waya tace itama bata san date d'in ba kawai watan ta sani, bayan Yaya Mubarak ya koma ya sanar masu yadda sukai k'arshe aka sa bayan ta gama Makarantar da sati biyu kawai, nan kowa ya amince aka hau Addu'oi da fatan Alkhairi, kud'i suka bada miliyan d'aya na neman aure da kuma kayan saka rana don basu taho da komai ba, anan parlon suka yi jam'in sallar Azahar gaba d'aya harda security d'in bayan sun gama aka shiga yin sallama su Aunty Mareeya ma duk suka zo suka yi masu sallama da godiya da kuma Addu'oin Allah ya maida su lafiya suna fara'a suke amsawa suka ce sai Allah ya kaimu biki kuma, tare duk suka fita dasu iyayen Fauzyn maza aka shiga k'ara yin sallama daga baya suka tafi, Aunty na komawa cikin gidan ta kira Fauzy lokacin tana zaune a saman gadonta tayi zuru tun bayan da aka kirata aka tambayi date d'in da zasu gama Makaranta gaba d'aya taji jikinta yay wani irin sanyi, lokacin da kiran Auntyn ya shigo har saida gabanta ya fad'i, hannunta har d'an rawa yake ta d'aukko wayar, tana yin picking Aunty ta rangad'a wata uwar gud'a tana fad'in Allah ya yarda an saka ranarta da Sameer suna gama Makaranta da sati biyu, runtse ido Fauzy tayi ta d'an cize baki Aunty tace bazata yi magana ba ko bata farinciki kawai sai ji tayi ta fashe mata da kuka, shewa Aunty tayi tace "yi kuka Fauziyya kin cancanci ki yi kukan farinciki" fad'i mata kud'in da suka kawo tayi cikin Muryar kuka ta tambayi yaushe zata dawo tace gobe in Allah ya kaimu, sauran yan gidan ne suka shiga amsar wayar suna mata Allah yasa Alkhairi harda gwaggo da Mahaifiyar ta, bayan sun gama wayar falon Baban suka koma baki d'ayan su harda iyaye mata aka cigaba da farinciki su Aunty suka sassauko da kayan Abincin nan cikin parlon kan Carpet aka cigaba da shagali don ba laifi sunyi abubuwa da d'an yawa kuma duka kad'an bak'in nasu suka ci, To Alhamdulillah sai fatan Allah ya nuna mana Auren Fauziyya da Sameer.......

92

_ASM BY ZAINAB BATURE_



~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~



.......A jiya Friday Haisam ya tafi Abuja daga can zai koma Us, lokacin da Fauzy ta kira Fatuu ta sanar mata da zancen saka ranarta tana a zaune parlon Hajiya, wata uwar k'arar murna ta saka ta hau yarfa hannu tana fad'in "Wayyo dad'i k'awata na taya ki murna wllh Allah ya sa Alkhairi ya kaimu lokacin da rai da lafiya" sai faman murna take ta kasa rufe baki, bayan ta gama wayar Hajiya ta tambayi abunda ya faru Fatun ta fad'i mata itama sosae tayi mamakin jin zancen Sameer zai auri Fauzy daga baya ta tayata murna tayi fatan Alkhairi, kiran gwaggo Fatuu tayi cike da Farinciki ta sanar mata dama tasan da Maganar itama murna ta tayata tayi fatan Alkhairi da Addu'oi,

Washe gari lahadi da yamma Aunty Mareeya ta dawo gaba d'aya bakinta bai rufuwa harda kudin da zasu siya kayan da zasu raba ma mutane aka bata, a ranar da daddare Mijin Aunty ya fita dasu suka je wani shopping mall dake kusa dasu suka siyo haddadun manyan biscuits dasu sweet kala kala da chocolate dama ta taho da goro da aka Siya acan Funtua, Washe gari bayan sunje Makaranta Fauzy taba Fatuu kayan ta raba ma mutane amman tace kada ta fad'i wanda zata aura haka Aunty Mareeya tace, sai bayan da aka yi masu break sannan ta rarraba ma yan ajin tana fad'i masu kayan sa rana d'in Fauziyya Ahmad ne akai ta mata Allah yasa Alkhairi harda yan ajin kusa dasu aka rarraba mawa, bayan an gama rabon ne Zainab tazo seat d'in su ta zauna a saman desk tace ma Fatuu amman da gani itama Fauzy dai mai kud'i ne zata aura ko, dariya Fatuu tayi tace miyasa tace haka tace ai ita tunda take bata ta6a ganin an raba irin wannan kayan a saka rana ba kana cin biscuit kunnan ka na motsi har saida ta ba Fauzy dariya, magiya ta hau yi ma Fatuu kan wai ta fad'i mata waye zata aura tana murmushi tace mata d'an uwan mijinta ne, zaro ido Zainab tayi tace bayan k'anwarta da zata auri k'anin shi itama Fauzy kuma d'an uwan shi zata aura tace mata eh cousin d'in shi ne, langa6ar da kai Zainab tayi ta marairaice fuska tace "Wayyo ni Zainabu baiwar Allah ni shine ban samu ko mai aikin gidan ba duk da ba son shi zan yi ba, Don Allah Fateema Ard'o nima ku samo man d'an uwan mijin naki" tana rufe baki Fauzy dake dariya tace mata basu son bak'ar mace sai fara Fatuu kau mi zatayi in ba dariya ba Zainab d'in tace abu mai sauk'i ai hakan ba abu ne mai wuya ba sai ta koma farar, Fauzy ta sake cewa to ai basu son farin bleaching, haka tay ta tsokanar Zainab d'in. Saida aka saka ranar da kwana ukku sannan suka yi waya da Sameer shima ita ta kira shi don ta gaishe shi kuma ko Maganar saka rana d'in bai mata ba har suka gama wayar a fili ta furta lalle akwai aiki a gabanta.

After a Month.......

lokacin cikin Fatuu ya shiga wata na shidda sai lokacin ta fara laulayi sosae, ba komai take ci ba yanzu ga amai da

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login