Showing 444001 words to 447000 words out of 512766 words
Chapter 149 - Asanadin Makwabtaka Book 3 Hausa Novel Complete
Unknown
27 Dec 2024
1676
serving spoon sai Warmers guda biyu Aysha ma na biye da ita da wasu kulolin abincin Masu kyau babba da ƙarama suka aje a saman carpet bayan Yadikko ta miƙe tay ma Fatuu alamar tazo ta nufi ƙurya Fatun tabi bayanta, bayan sun shiga tace mata yanzu ya za'ai Haisam ya saba cin abinci a saman table gashi babu wai ko a ɗauki drawer ɗin gado sai a ɗaura mashi sama Maganar dariya taba Fatuu tace mata ai lafiya lou yana ci a ƙasa Yadikkon ma dariyar take tace yauwa to shikenan,
"Baki tambayi Mino ba" Fatuu ta faɗa tana murmushi, ɗan yarfa hannu Yadikko tayi tace tana son ta tambaya wai kada aga tayi rashin kunya ta tambayi tana lafiya ita da mijin nata Fatuu tace eh sunyi waya ta gaya mata zasu zo harda cewa wai don Allah a taho da ita tace waye zai yi wannan haukan duka sati guda da yin aure ta marairaice mata kaman zata yi kuka tace ai ko kukan jini zata yi bazasu zo da ita ba, Yadikko dake dariya tace ai lalle kam kafin da sauri tace taje ta zuba ma Haisam Abincin tace to ta juya ta fita, miƙewa Baffansu yay yace ma Aysha taje tace ma Yadikko ta zubo ma wanda ya kawo su abinci sai ta kawo mashi waje tace to yace ma Haisam bari ya barsu suci Abinci Fatuu ta kalleshi tana mashi murmushi shima shine akan fuskarshi ya juya ya fita, a saman carpet suka zauna Fatuu tay serving nasu abincin wanda shinkafa da miya ne sai kuma burabusko sai gasassun zabbi cikin miyar abincin an cacca6a nama sai uban ƙamshi ke tashi, ba laifi Haisam yaci abincin sosae ba kamar burabuskon yayi mashi daɗi harda ce ma Fatuu bata ta6a yi masu irin shi ba tay yar dariya tace tunda yayi santi daga yanzu zata rinƙa yi yay murmushi ba tare daya ce komai ba su twins ma da alama yayi masu daɗi sai cin shi suke Aysha na daga gefe tana ba Adam ita kuma Fatuu tana ba Abie, bayan sun gama Aysha da Fatuu suka kwashe kayan suka kai Kitchen bayan sun dawo cikin parlon Yadikko ta fito masu da Fura a cikin jug dama ita take haɗawa a cikin ɗaki da kanta ta zuba ma Haisam yana ɗan murmushi yace mata ya ƙoshi yaci abinci sosae tace ya zai zo ruga bai sha fura ba yace to a bari kafin ya tafi zai sha jin haka yasa da sauri tace wai badai yau zasu koma ba cikin cool voice ɗin shi yace a'a shine zai koma Yola ita tana nan sai gobe zai dawo su tafi tace yauwa to Aysha ma ta washe bakin murna, miƙa ma Fatuu furar data zuba tayi tace ita to tasha ta amsa Aysha tace a zubo wata taba Adam, sosae Furar tayi daɗi don harda zuma aka sa ga dawon sabo ne haka nonon ma Fresh ne Fatuu nasha tana ba Abie duk ya 6ata saman bakin shi da ita harda su tanɗe baki yana yin ɗan sauti sai dariya yake basu cike da tsokana Yadikko ta kai hannu tace a bata furarta tunda bai yarda da mutane amman ya iya shanye masu abu yana ganin Fatuu ta miƙa mata cup ɗin ya fara ta6e baki zai saka kuka da sauri Yadikko ta maido mata tana dariya tace sak irin yadda take kuka da ƙuruciyarta haka suma suke yi Fatun tay murmushi ta ɗan saci kallon Haisam suka haɗa ido ya ɗan yi murmushin gefe tare da juyar da idon shi, Fatuu ce ta tambayi Yadikko ba'a samun wuta ne taga sai generator aka kunna tace wutar lantarkin ce ke yawan samun matsala daga can titi da aka jawo ta in ta lalace sai su daɗe babu ance wai ko zata daidaita sai ansa transformer anyi babban aiki ta jinjina mata kai, Baffan su Fatuu ne ya dawo yace ma Haisam ya fito yayi alwala lokacin salla ya ƙarato yace to tare da miƙewa ya kaishi ɗakin shi da shima yake tsab ga toilet a ciki ya nuna mashi yace akwae ruwa aciki zai jirashi a ƙopar ɗaki, a ƙopar gidan inda aka saba yin salla sukayi bayan angama akai ta gaisawa da Haisam ana ma mutane bayanin ko wanene daga baya suka dawo cikin gidan tare da Baffa lokacin Yaya da Mero da sauran manyan mata iyaye suka shigo gaisawa dashi Yaya nata washe baki tace ai sun bari su huta ne su twins dai sai dae a kalle su, wuraren ƙarfe ukku Haisam yace ma Fatuu yana son suje gidan Alhaji Lawal su gaisa dashi sai a maidota shi kuma ya wuce tace to, shiryawa tayi ta canza kaya su twins ma ta canza masu sannan suka tafi harda Aysha ta riƙe Adam. Lokacin da suka je Alhaji lawal ɗin na nan da yake Weekend ne sosae suka nuna farincikin ganinsu a falon Alhaji lawal aka saukesu Hajiya Rabi'atu na murmushi tace wannan zuwan bazata haka ba'a sani ba balle a shirya tarbarsu sosae suna murmushi suka ce mata ai ba komai, ruwa da lemu da Abinci aka kawo masu duk suka ce a ƙoshe suke Alhaji Lawal yace bai yarda ba ya za'ai suzo gidan shi suƙi cin abinci ƙarshe saida suka ci kaɗan, koda Alhaji Lawal yaji zancen tafiyar Haisam Yola sai yace ya bari mana su kwana gaba ɗaya anan gidan sai shi driver daya kawo su ya koma tunda nan akwae driver koda zasu buƙaci fita, da yake Haisam ɗin bai cika son kwana ba tare da Babynshi ba sai dole gashi kuma sun nuna suna son ya kwana bazai iya gardama masu ba sai ya amince da hakan, bayan anyi sallar La'asar Alhaji lawal yace ko zasu zagaya suga gari driver ya kai su Haisam ɗin yace ba sai Driver ya kaisu ba bari yay driving ɗin da kan shi, cike da zolaya Alhajin yace kada fa ya 6ace a garinsu Senator ya turo masu bataliyar sojoji Haisam ɗin yay dariya yace bazai bace ba tunda yana tare da yar gari, tare da Fatuu da Aysha suka fito Haisam ne ke tuƙa Motar suka shiga cikin garin Jumeta, bayan sun zagaya garin can da Yamma suka nufi ruga, lokacin da suka shiga garin makiyaya mata da maza cikin shiga ta fulani nata dawowa daga kiwo suna sanye da kayan fulani dabbobi ko ta ina suna ta 6ullowa, juyawa Haisam yay ya kalli Fatuu da turanci ya tambayeta itama tayi irin haka tay dariya tace ita fa yar lelen Baffanta ce duk irin wannan abun bai bari tana yi ko tallar Nono da yan matan gidansu ke yi lokacin ita bata taba yi ba, murmushi yay idon shi akan hanya yace ai ko don kada ta jawo mashi rigima ya hana tayi Fatun ta kyalkyace da dariya, ta bayan gidan su tasa su bi tace zata nuna mashi ƙoramar dake wurin, bayan sun je wurin parker Motar yay duk suka fito suka shiga zagaya wurin ruwa nata gudana ga wani irin ni'imtaccen sanyi ga bishiyun kayan itatuwa da sukai ma wurin ƙawanya duk sun nuna gasu ƙasa ƙasa Fatuu tace bari ta tsinko masu Haisam ɗin ya hana tasa Aysha ta tsinko masu itama yace ta bari kada wani abu ya cije ta tana dariya tace mashi ai suna zuwa ba abunda ke samun su sannan ya bari, basu daɗe a wurin ba harda hotuna yay masu suka tafi saboda yamma tayi sosae, wata hanya Fatuu ta nuna mashi tace su bi nan zasu 6ullo ta ɗayan gefen gidan, suna zuwa wani wuri jikin gidan nasu da sauri ta ɗaga hannu tana nuna mashi wurin tace ya ganshi ya ɗaga mata kai tace to a daidai nan ne ta ta6a yin shuka har ta jefe ma Jibo Akuya har baisan lokacin da yay dariya ba har haƙoranshi suka bayyana don ta tuna mashi ranar data bashi labarin Akuyar itama dariyar take Aysha dai bata san akan mi suke magana ba, lokacin da suka iso gidan ƙopar gidan cike yake da mutane wurin sai kace yar yara, bayan ya parker Motar suka fito cikin mutanen da ke zaune a ƙopar gidan harda Baffa da yau yaƙi zuwa ko ina saboda zuwan su suka taso suka tarbesu Fatuu da Aysha suka wuce ciki shi kuma a nan ya nuna zai tsaya shima aka bashi wurin zama bayan sun shiga ne Fatuu ke faɗi ma Yadikko zancen kwanan da zasu yi a gidan Alhaji Lawal, anan sukai isha suka ci Abinci harda wata sabuwar Fura aka dama masu mai sanyi sai gashi duk sun fi shan furar ma akan Abincin shima Haisam sosai tayi mashi daɗi su twins kau ba'a Magana hannu bibbiyu suka ruƙe cup suna sha duk sun ƙara yi ma bakin su dama dama sai tanɗan baki suke ana dariya sai gashi suma an sasu yin dariyar Yadikko har tana ce ma Fatuu kodai bata basu Fura ne tace mata eh gaskiya don lokacin da suka fara cin abinci basu ƙasar sai da suka zo bikin nan kuma lokacin da aka sha Furar a gidan Gwaggo basu gidan Yaddikon tace to gaskiya a rinƙa basu tunda dai sun gani da idon su suna so, kallon Haisam Fatuu tay ta tambaye shi a US ana samun Furar kuwa ya bata amsa da baza'a rasa ba tunda ana samun abubuwan mu na nan sosae saboda akwae mutanen mu acan shima Furar ba'a rasa masu yin shi suna saidawa in suka koma zai bincika Yadikko tace yauwa gaskiya asamo ma angwayenta Fura harda cewa don ma nesa bata maganin kusa ai da ta rinƙa yin Furar tana aika masu can don tasan koda an samu sai tata tafi daɗi duk sukai yar dariya, wurin ƙarfe takwas da rabi suka fito zasu tafi gidan Alhaji Lawal Fatuu ta ɗaukko jakar kayanta sukai sallama dasu kan sai gobe, har bakin Mota Baffan su Fatuu ya rako su har yana ce ma Haisam zai gane hanya cikin daren nan ko ya rakasu sai ya dawo yana murmushi yace mashi lafiya lou zai gane yayi mashi godiya sukai sallama, suna kan hanya ne Fatuu ke tambayar shi yanzu ya za'ai baida kayan baccin da zai saka tunda kayan shi na Yola yana murmushi yace mata sai ta bashi cikin nata yasa ta kyalkkyace da dariya tana faɗin in yana so sai ta bashi in dai zasu shigeshi, tun akan hanya su twins sukai bacci Fatuu na dariya tace Fura tayi aiki yay murmushi, bayan sun iso a harabar gidan suka iske Alhaji Lawal ɗin zaune kan kujera hannun shi ruƙe da Jarida yana ganin su ya taso ya nufo Motar bayan duk sun fito yana murmushi yay masu sannunsu da dawowa yace ai zaman dakon jiransu yake don da basu dawo ba yanzu bin sahun su zai duk sukai dariya tare da gaishe shi, tare suka shiga cikin gidan Hajiya Rabi'atu ta tarbesu, a part ɗin baƙi aka saukesu yana da parlor da kuma Bedroom an gyara masu shi tsaf sai ƙamshi da sanyin Ac ke tashi Hajiya Rabi'atu ta nuna masu kayan abinci da aka jere kan dining table tace gashi nan sai suci in sun huta harda tambayar ko a turo wadda zatai Serving nasu Fatuu tace a'a lafiya lou zatayi, duk da ba wata yunwa suke ji ba saida suka ci lafiyayyun abincin da aka yi masu saboda ɗazun da suka zo basu wani ci sosae ba, suna cikin cin Abincin Alhaji Lawal ya shigo cikin parlon hannunshi ruƙe da wata babbar farar jakar siyayya ya nufi kan kujera ya aje daga nan inda yake yace ma Haisam gashi nan yayi amfani dasu yace to tare da yi mashi godiya, bayan sun gama cin Abincin ya duba kayan ciki wanda kayan bacci ne kala biyu na maza sai kuma ɗinkakkun shaddoji suma kala biyu farare da brown kamar Alhajin yasan irin dinkin da yake so don gaba ɗaya kayan irin ɗinkin ne sai wasu yan ƙananun kwalaye guda biyu nan kuma agoguna da links ne a ciki harda biro akwae kuma kwalayen turarurruka guda biyu gaba ɗaya kayan sunyi kyau da ganin ba ƙananun kaya bane, bayan sun gama duba kayan ya kalli Fatuu cikin cool voice ɗinshi yace ba rabon yasa kayan baccinta kenan ta faɗa jikinshi tana dariya ya haɗa da ita da ledar ya sunkuceta suka nufi Bedroom.
Washe gari misalin ƙarfe goma saura gaba ɗayan su sunyi wanka suna parlon Alhaji Lawal suna yin Breakfast tare Fatun na ruƙe da Abie Hajiya kuma na ruƙe da Adam ta samu yanzu ya yarda da ita dama shi in dai zaku wuni tare to zai fara yarda da kai, baka jin komai sai ƙarar cokulla sunyi nisa a cikin cin Abincin suka ji anyi sallama cikin parlon a kusan tare duk suka kalli entrance, wani irin bugu gaban Fatuu yay da tayi arba da wanda ya shigo ba kowa bane face Khalid yana sanye da ƙananun kaya idanunshi na sanye cikin farin glass irin nasu na likitoci har yanzu dai yana nan yadda yake bai yi ƙiba ba, da sauri ta kauda idonta daga barin kallonshi ya nufo dining area ɗin yana ta sakin ƙamshi, bayan ya ƙaraso a gefe ya tsaya kusa da Dad ɗinshi ya gaishe da shi ya amsa tare da ce mashi yazo lafiya da tambayar iyali duk ya amsa mashi kafin ya kai idon shi kan Hajiya yana ɗan murmushi ya furta "Mom, Good Morning" itama murmushin take ta amsa mashi tare da tambayar Matar shi da kuma ɗiyar shi Zarah ya amsa mata da suna lafiya suna gaishe ta, tace maimakon ya taho masu da Zarah still murmushi yake yace lokacin da zai taho bata tashi ba ta jinjina kai, a cikin ran Fatuu ta shiga maimaita sunan ɗiyar shi da aka faɗa tana kokonton dalilin saka sunan, Alhaji ne ya nuna mashi Haisam da idon shi na kan Abincin gabanshi kamar bai ma ji shigowar Khalid ɗin ba yace mashi "ga baƙon mu mijin ɗiyata Fateema" kai ya jinjina Alhaji ya kalli Haisam yace mashi ga babban ɗan shi Khalid su gaisa sai lokacin ya ɗago fuskar shi a sake kafin yace wani abu Khalid ya miƙa mashi hannu ya aje cokalin hannunshi shima ya bashi nashi suka gaisa yayi mashi anzo lafiya Haisam ya amsa mashi da lafiya lou, bayan sun gama gaisawar maida idon shi yay kan Fatuu da taki ɗago kai ta kalle shi ya furta "Fateema an zo lafiya" damm gabanta ya faɗi ta haɗiyi abu saida tay ƙoƙarin daidaita natsuwarta sannan ta ɗago tana yin ɗan ƙaƙalallen murmushi ta gaishe dashi da ƙyar ya amsa don saida gabanshi ya faɗi ganin yadda ta koma saidai bai bari an fahimci wani abu ba, tana gaishe dashi da sauri ta janye idonta daga kanshi, kallon Abie dake hannunta yay yace "Wannan yaran mu ne?" kafin ta bashi amsa Mom ɗin shi ta riga ce mashi eh twins ne ta nuna mashi Adam dake hannunta ya jinjina kai tare da kai hannu zai amshi Adam da yake Mom ɗin na kusa dashi Adam ɗin ya ƙanƙameta alamar bazai je ba Mom tace mashi suna yin ƙyuya ne sai sun saba da mutum suke yarda ya ɗaukeshi yana murmushi ya furta Ok, Dad ɗinshi ne ya nuna mashi seat da ba kowa yace yay joining nasu yasan ƙilan bai yi Breakfast ba tunda da wuri ya taho, gaba ɗaya Fatuu ta takura zaman Khalid a wurin da ƙyar take cin Abincin can ta saci kallon Haisam taga idon shi na kan Abincin gabanshi tana son ta gane yanayin fuskar shi amman ta kasa, Khalid bai daɗe da zama ba Haisam ya miƙe duk suka kalle shi Alhaji yace badai har ya ƙoshi ba yana murmushi yace mashi eh yace to amman ai kamar bai ci sosae ba still da yanayin murmushi ya bashi amsa da yaci da yawa Alhajin yace shikenan ya manta ma Yan gayu basu cin Abinci sosae Haisam ɗin yay yar dariya haka ma Hajiya Rabi'atu Khalid kuma murmushi yayi Fatuu kam bata ma ɗago ba balle aga yanayin fuskar ta, bayan tashin Haisam wurin duk sai taji ta ƙara takura sau biyu tana satar kallon Khalid taga ita yake kallo abunda bata sani ba dana sani kawai yake acikin ranshi don ganinta ya fama mashi babban tabon sonta dake cikin zuciyarshi sai kallon su twins yake yana raya ƙilan da yanzu su yaranshi ne, gaba ɗaya Abincin ya fice ma Fatuu arai haka shima Khalid ɗin ba don yana jin daɗin shi ba yake ci, Haisam bai daɗe ba da tashi itama ta miƙe Dad yace wato Romeo ya ƙoshi shine itama Juliet zata tashi Fatun tay yar dariya kafin tace ta ƙoshi ne, cikin parlon ta nufa inda Haisam ke zaune yana latsa waya, Bayan sun gama cin Abincin gaba ɗaya a falon aka zauna ana hira jefi jefi Haisam ke saka baki anan ma Fatuu ta lura da yadda Khalid ke fakaitar idanun mutane yana kallonta cikin sa'a bayan ɗan wani lokaci Abie yay bacci ta miƙe tace zata je ta kwantar dashi, bata daɗe da tafiya ba shima Adam yayi baccin Hajiya ta bita dashi ya rage saura Alhaji da Khalid sai Haisam suka cigaba da yin hira wadda yawanci akan aikin su ne suna cikin haka Haisam ya roƙi Khalid kan yana son ya shige ma su Baffan Fatuu gaba zasu kai Arɗo Asibitin da yake aiki a duba shi sosae yace mashi ba matsala, suna zaunen har lokacin sallar Azahar yayi Dad yace suje suyi kafin su tafi Haisam ya kira Fatuu a waya yace ta shirya da sun dawo daga salla zasu je can ruga suyi bankwana dasu sai su koma Yola ƙarfe biyar jirginsu zai tashi zuwa Abuja tace to, suna dawowa sallar ya sanar ma Dad zancen zuwa rugar yace Ok amman zasu dawo ta nan ko sai Driver ya kai su Yola ɗin Khalid na jin haka yace bari suje rugar tare sai ya duba jikin arɗon in