Showing 345001 words to 348000 words out of 512766 words

Chapter 116 - Asanadin Makwabtaka Book 3 Hausa Novel Complete

Unknown   

27 Dec 2024

2401

ta d'ago ta kalli Fatun sai kuma ta juya ta kalli Aunty dake niyyar tambayarta minene ta rigata ta hanyar d'aga mata wayar tana nuna mata credit alert d'in, waro ido itama tayi ta hau girgiza kai "gaskiya Zarah kud'in nan sun yi yawa a rage don Allah hidindimun rayuwar nan da yawa daga wannan fa sai wannan" girgiza kai Fatuu tay tace Allah ko an maido mata itama sai ta sake turowa, ba yarda Aunty bata yi da ita ba amman tace Allah baza'a rage ba ai don tana da su ne ta bada kuma in tasan zata k'waru ai bazata bada har haka ba inda ma tana dasu sosae fin haka zata bada to don ta tura ma Baffan ta wasu ya k'ara jari sannan kuma an siya mata shanaye, gaba d'aya fuskokin su sun nuna damuwa tana dariya tace don Allah wai ba an zama d'aya bane kuma itama ai ba wahala tayi ta same su ba nan ta shiga fadi masu da bikinta ta samu kud'i sosae don ko Mahaifiyar Sameer d'in 500k ta tura mata banda wanda k'awayen Mom suka babbata mai dubu hamsin mai dubu d'ari, daga baya godiya suka shiga yi mata Fauzy ta rungumeta ta saka kuka tana fad'in bata san da wane baki zata mata godiya ba tabbas dama tunda ta fara ganinta a school taji tana kaunarta ashe ita d'in Alkhairi ce a gareta, murmushi kawai Fatun ke yi tana ce mata haba ba komai fa,

"In rungume ku to nima in yi kukan" Aunty ta fad'a ta kai hannu ta rungumo su gaba d'aya Fatuu ta saki dariya, bayan ta sake su sosae tayi ma Fatuu godiya da Addu'oi daga baya ta mik'e tace bari taje suyi magana da Yaya Mubarak d'in, har ta juya Fatuu ta kirata ta juyo fuskarta da murmushi ta tambayeta ya akai ta d'an yamutsa fuska tace Abincin data dafa take son ci, hannu Aunty ta kai ta ruk'e ha6a tace "wani aikin sharri sai ciki, yanzu ki kawo mana wannan had'addan Abincin amman namu tagajan tagajan kike son ci" gaba d'aya sukai dariya Fauzy tace wllh ta manta ne bata zubo mata ba tunda tazo ko ruwa ma bata kawo mata ba Aunty tace gaskiya bata kyauta ba wato ta dafi abincinta mai dad'i kuma ita ko ruwa bata kawo mata ba hakan ai ba Adalci bane, da sauri Fauzy ta saukko tana fad'in ayi hak'uri tasan tayi ba daidai ba bari ta kawo mata suka nufi k'opa tare da Aunty,

bayan taje Bedroom d'inta nan ta hau fad'i ma mijinta Abban su Hanif yadda sukai da Fatuu game da bayanin da Haisam yayi kan Sameer da yadda sukai da Mahaifinta harda kud'in da Fatun ta bada, sosae yaji dad'in dukkan bayanan dama jiya da daddare Aunty ke fad'i mashi yadda sukai da Baban su, godiyar kud'in da Fatuu ta bada yay da Addu'ar fatan Alkhairi, kiran yayan nasu ta shiga yi bayan ya d'aga sun gaisa yace mata ai gashi ma a gida yanzu Baban su ke fad'i mashi yadda sukai yanzu ma suna niyyar kiran su Mutanen da suka kira din ne tace to duk yadda sukai dasu sai ya sanar mata, har zata mashi sallama yace mata ta dai tabbatar da duk bayanan da aka bada kan shi gaskiya ne ko don kada aga yana da nasaba ayi abunda za'a zo ayi dana sani daga baya ba fata ake ba, halin Haisam ta shiga fad'i mashi harda yadda ya auri Fatuu shima duk da ba ajin auran shi bace ta kuma tabbatar mashi da yadda yake ruk'e da ita yanzu daga baya ma sai ta mik'a ma mijin nata wayar don ya k'ara mashi bayani yana d'an murmushi ya amsa, bayan sun gaisa a nutse ya shiga yi mashi bayanin gaskiya Haisam mutumin kirki ne tun daga kan mahaifin shi da dangin shi yace yana da yak'inin bazai fad'i abun da ba haka bane akan d'an uwan nashi, hamdala Yaya Mubarak yay yace dama haka suke son ji tunda bai kamata ba ace ba ai wani bincike ba akan shi saboda aure ba abun wasa bane bayan sun k'ara tattaunawa daga baya sukai sallama ya mik'a ma Aunty wayar, cigaba da tattaunawa kan abunda yakamata ayi sukai daga baya sukai sallama.

Bayan sallar Magrib Aunty ta shigo d'akin Fauzy lokacin Fatuu na zaune akan abun salla cikin washe baki ta sanar masu yanzu Yaya Mubarak ya kirata yana sanar da ita an kira wurin su Sameer din yadda aka fad'a yayi masu sun ce ranar Asabar zasu je Funtua har saida gaban Fauzy yay wani irin bugu jin abun dai da gaske ne gashi ko waya da Sameer d'in ma basu yi ba, sosae Fatuu tayi murnar jin hakan sai faman washe baki take haka Aunty Mareeya ma da alama ta manta da zancen rocket, kiran Mahaifiyar su tayi tace mata ga Zarah d'in dama suna gaisawa da ita ta wayar Fauzy, cikin girmamawa kaman ko yaushe Fatuu ta gaishe ta bayan ta amsa ta tambayi su gwaggo da mai gidan nata duk tace mata lafiyar lau nan ta hau yi mata godiya da Addu'oi Fatun na murmushi tace mata ai ba komai duk an zama d'aya tace hakane kam. Bayan sallar isha Tk ya kirata yace gashi nan kopar gida ya zo tace to dama a shirye take don sunyi waya da Haisam yace mata ga Tk d'in nan zuwa, hijab Fauzy ta saka suka fito a tare, a cikin parlon suka iske Aunty Mareeya tana serving mijinta Abinci da Hanif shida k'annan shi guda biyu sultan da iman, tana ganin su tace badai tafiya ba Fauzy tace eh ga Tk nan yazo shi zai maida ta, mik'ewa tay tana fad'in maimakon to ya shigo, gaisawa sukai da mijin Aunty d'in yana d'an murmushi ya amsa tare da yi mata godiyar abun Alkhairi daya ji itama murmushin take tace mashi ba komai, Bedroom Aunty ta nufa bada Jimawa ba ta fito ta yafo gyale Fatuu tay ma mijin nata sallama yace ta gaishe da maigidan ta, harda su Hanif suka mik'e don yi mata rakiya, har zasu fita daga parlon Aunty tace ma Fauzy to ina basket d'in Abincin da sauri tace au ta manta wllh ta koma don ta d'aukko su kuma suka fita.

Bayan Fauzy ta gama komai ta kwanta ta fad'a duniyar tunanin Sameer, a yanzu ta gane tana son shi don da kafin suji bayani game dashi fargabar kada ace yana da wani mummuna hali ce ta kamata amman yanzu tunda taji bayanin da Haisam d'in yay take jin wani irin farinciki a cikin ranta sai faman yawo Sameer d'in yake mata a rai tun ma Fatuu na nan, hannu ta kai gefen filon data d'aura kanta ta d'aukko wayarta, bayan ta bud'e gallery ta shiga ta bud'o hoton shi ta k'ura ido tana kallo, zuciyar ta ce ta shiga raya mata in dai ta aure shi tabbas ba K'aramin dace da sa'a tayi ba wllh don ta ko ina Sameer yafi k'arfinta nesa ba kusa ba, shiru tayi tana cigaba da kallon hoton fuskar ta da d'an murmushi a zuciyarta ta shiga fad'in "da gaske kana sona ko kuwa matsayin taimakona zaka Aure ni" shiru tay don bata da amsar da zata ba kanta, tana ta faman zooming hoton tana k'are mashi kallo ji take kaman ta kira shi don sai taji tana son jin muryar shi, a ranta ta raya to in ma ta kira shi d'in tace mashi mi wata zuciyar tace ta gaishe dashi kamar yadda take yi, kokonton kiran nashi ta shiga yi k'arshe ta yanke bazata kira shi ba gaskiya kada yay tunanin ko don Saboda Maganar neman auren nata ne yasa ta kira, "to kuma in ba ki kiran nashi taya zai sake maki har ku saba tunda dai shi ga irin halin shi, kamata yay ki fara k'ok'arin jawo shi a jiki yadda zai sake maki har kiyi abunda Ya Haisam yace na raba shi da matan dake bibiyar shi" zuciyar tace ta raya mata hakan tay shiru tana ta d'an cizon k'umbar babban yatsanta gani take kaman hakan ba abu bane mai sauk'i can dai ta fita daga cikin gallery d'in ta koma phone bayan ta nemo number d'in shi saida tay d'an jimm kafin tay dialing nan take ta shiga, duk bugu d'aya tare yake da fad'uwar gabanta sosae fargabar kiran shi ta kamata yau ba kamar sauran lokuttan da ta kikkira shi ba a baya, har ta yanke bai d'aga ba sam bata ji komai ba don dama duk in ta kira bai d'auka sai daga baya ya biyo kiran, tun tana saka ran zai kira har ta fara fiddawa ta shiga sak'a ko bai son yin magana da ita ne ko kuma k'ilan wani uzurin yake k'arshe kuma ta yanke k'ilan ma yayi bacci ne, rufe idanunta tayi da niyyar yin bacci bayan ta gama Addu'a bata dad'e da rufe idanun ba wayarta ta fara ringing har saida gaban ta ya fad'i da sauri ta bud'e idanun, k'ura ma screen d'in ido tay bayan ta d'aukko wayar tana kallon sunan Sameer daya bayyana kaman bazata d'auka ba can dai a d'arare tay picking ta kai wayar kunnanta, shiru tayi shima kuma bai tanka ba can murya k'asa k'asa tace mashi ina wuni taji ya amsa da "lafiya" d'an murmushi ta saki jin voice d'in shi, tambayarta yay mi take bata yi bacci ba cikin daidaita natsuwa ta bashi amsa da ai ta kwanta baccin ne dai bai zo ba, bai ce komai ba suka d'an yi shiru can ya sake tambayar tana ina ne ta bashi amsa da tana gidan Sister d'inta tazo weekend k'asa k'asa taji ya furta Ok,

"Kai ma kayi baccin ne?" da k'yar ta tambaya harda d'an cize baki, amsa ya bata da eh acikin baccin ne suke magana nan take ta gane Magana ya gaya mata ta saki yar dariya da har saida yaji sautin ta tace "ai ina nufin ko kayi bacci ne na tashe ka,

"No, ina wurin Dad ena" d'an waro ido tay bata ce komai ba suka k'ara yin shiru, "akwae wani abu?" bayan d'an wani lokaci taji ya tambaya da sauri tace "a'a, dama na kira in gaida ka ne",

"Sai kin ga dama kike wannan kenan" ba zato taji yace haka ta d'an waro ido a ranta tace kaji shi ma ba sai ya ga dama yake kirana ba a fili kuma sai tace "a'a, ba haka bane, ina son in rink'a kiran to kuma ban san ko kana cikin aiki ba kada in takura maka,

"You can call whenever you want, in ina free zamu yi magana" bayan ya d'an yi shiru taji ya fad'i hakan wani irin dad'i taji tana murmushi tace mashi to,

"Yaushe zaki gama School?" d'an jimm tay alamar tunani kafin tace "nan da Kusan 7 Months masu zuwa" shiru ya d'an yi sai kuma taji yace Kusan ko kuma ya kai da sauri tace eh zasu yi good 7 Months kafin su gama ya furta Ok, shiru suka k'ara yi Fauzy sai faman sakin k'ayataccen murmushi take don wani irin dad'i take ji da suna wayar duk da ba wata Magana suke ba, bayan wani lokaci taji yace mata ta kwanta yadda zata tashi da wuri tace ai gobe ba School ya furta Ok ya manta,

"Yaushe zaka koma UK wurin aikin ka?" kawai sai ji tayi ta furta hakan da bud'ar bakin shi sai ce mata yay ya akai tasan a can yake aiki, waro ido tay ta bud'e baki don sai lokacin ta ankare da tayi 6aram6arama da ta fad'i hakan yanzu ya zata ce mashi yadda akai ta sanin tunda bai yuwuwa tace a wurin Haisam, tana haka taji yace yana jiran ta bashi amsa ta shiga yan kame kame can zuciyarta ta tuna mata da hoton shi data gani a Dp tare da turawa kuma akwae rubutu a k'asan dp d'in duk da bazata iya tuna mi aka rubuta ba, cikin yar rawar murya tace "d..dama a profile d'in ka ne naga hakan" tana yin Maganar gabanta ya hau fad'uwa gudun kada ace ba hakan a profile d'in, cikin ikon Allah kuwa a business profile d'in shi akwae bayani akan Company d'in nasu hakan yasa ya furta "Ok" wani sanyi taji a ranta ta d'an yi farfar da idanu alamar ta sha, ce mata yay zai koma soon,
"Allah ya kaimu ya kai ka lafiya" slowly ya furta "Ameen", shiru suka d'an k'ara yi taji yace yana son yin bacci ya gaji ya za'ai da sauri tace "to, gud night" shima hakan ya furta mata ta ciro wayar ta kashe kiran, mirginawa tay ta koma kallon sama tana ta murmushi sosae abun ke bata mamaki wai ace wannan mutumin data gani a d'akin Ya Haisam taita kallon shi har ya Harare ta ne wannan kuma ma wai aure zasu yi, jinjina kai ta hau yi still da murmushi akan fuskar ta a fili ta furta "ikon Allah kenan!" komawa tay tunanin to wai bai iya soyayya bane ko mi ace wai a haka soyayya suke tayi ma tunanin zai mata Maganar neman Auren nata amman bai ce komai game da hakan ba, wata zuciyar ce ta raya mata k'ilan kuma izzar ce ta sa haka kaman yadda Aunty tace ko kuma bai sake mata ne suyi soyayyar don kada ta raina shi, yar dariya tay ta raya in hakane kuma zai aureta, tunanin to su matan da akace yana ta6awa ba soyayya suke ba can kuma ta raya koda yake ai ance yawanci sune ke lik'e mashi, yin wannan tunanin yasa taji ranta ya 6aci ta d'aure fuska a fili ta furta "zanyi iya bakin kokarina inga na hanaka aikata hakan in sha Allahu" ta kai Maganar tana d'an jinjina kai, wayarta ce tay k'ara ta juya ta kai hannu ta daukko, sak'o ne aka turo mata bayan ta bud'e bin alert d'in tay da kallo na 200k daga Sameer, d'an murmushi tayi ta fita daga wurin tasan ko ta kira ba d'auka zai yi ba hakan yasa ta shiga WhatsApp ta tura mashi sak'on godiya, tunanin ko Aunty Mareeya tayi bacci ta shiga yi sai kuma ta raya bari ta jaraba kiran ta, wayar na fara ringing ta d'auka tare da tambayar Fauzyn miye tace "ashe baki yi bacci ba, dama zan sanar maki ne yanzu muka yi waya da Sameer" tana rufe baki tace "da gaske...,ya kira kenan?" Shiru Fauzy ta d'an yi kafin tace mata a'a itace ta kira ta gaishe shi,

"Ya yi kyau hakan kin kyauta dama bai kamata ki biye ma halin shi ba ta hakane zaki rink'a jawo shi jiki har ya sake maki kuma ki cire duk wani tunanin wai ko zai aure ki ne don ya taimaka maki da sauran su in bai son ki ba yadda za'ai ya aure ki tunda aure fa ba abun wasa bane da zai tsallake tarin yan mata ya za6e ki don taimako ba gama misali nan akan Zarah ba haka mukai ta nuna mata mijin nata na son ta shiyasa ya amince ya aure ta kuma sai gashi hakan ne" jinjina kai Fauzy tay tace to,

"ya yi maki Maganar zuwa neman Auren naki ne" da sauri tace "a'a wllh bai ce man komai ba game da hakan kawai waya mukai nace na kira in gaishe shi ne shine har yace wai sai naga dama nike hakan nace ai don kada in rink'a takura mashi ne shine yace zan iya kiran shi duk in ina so in dai yana free zamu yi magana",

Aunty ta furta da kyau ko wannan ma ai alama ce ta yana son ta, cigaba Fauzy tay tace mata ya tambayi lokacin da zata gama Makaranta ma, a d'okance Aunty tace "ina jin Saboda ranar da za'a saka maku ne ya tambayi wannan to",

da sauri Fauzy tace mata eh itama tayi tunanin hakan don dama data kira bai d'auka ba sai daga baya shine yace mata yana wurin Dad d'in shi ne, "Ma sha Allah abu dai nata tabbata" Aunty ta fad'a tana washe baki, fad'i mata zancen kud'in daya turo yanzu tayi Auntyn tace "wato shi soyayyar bada kud'i ya iya bata kalamai ba kenan, hakan yayi kyau yayi ta turo su muna mashi godiya don yanzu ba zamu rink'a mamaki ba tunda mun fahimci kud'in ne har sun mashi yawa" Fauzy na dariya ta furta "kai Aunty...",

"Allah kuwa Fauziyya a yadda aka fad'i aikin da yake na tabbatar ba k'ananun kud'i yake samu ba ga kuma Baban shi Governor kacokam, da ya turo maki kawai kiyi mashi godiya tunda k'arshe ma shi za'ai ma amfani dasu" murmushi kawai Fauzy tayi kafin tace mata yanzu ta turo mata su gaba d'aya ne tace a'a ta bari sai gobe zasu zauna su tsara abubuwan da za'a yi dasu don har sun gama Magana da baban su Hanif ranar Alhamis zata tafi sai ta bar su sultan d'in a gidan Maman taufiq ranar Friday in ta dawo daga School sai su dawo wurinta Fauzyn tace to,

"Oh ikon Allah ikon gaske, abu dai kinga kamar wasa kuma tabbata zai yi in sha Allah, gaskiya had'uwar ki da Zarah babban Alkhairi ne yo ke wannan ai ko karatun naki ma ba lalle ki amfana da shi ba kamar yadda kika amfana da sanin Zarah kawai dai shi ya zama sila ne",

"Wllh Aunty baki ji yadda nike jin ta ba a raina tamkar yar uwata uwa d'aya uba d'aya, ji yadda ta d'auki uban kud'i ta bada d'azun dama kuma tana man hidima sosae wannan ai ko wani dan'uwan naka mai hali wllh ba lalle yayi maka hakan ba,

"Ai tsakanin mu da ita sai dai Addu'a kawai wllh itace zamu iya saka mata da ita amman duk da hakan ina fatan ace munyi mata wani abu da zata ji dad'i sosae a ranta......" Da sauri Fauzy ta katseta

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login