Showing 375001 words to 378000 words out of 512766 words
Chapter 126 - Asanadin Makwabtaka Book 3 Hausa Novel Complete
Unknown
27 Dec 2024
1643
ido sai sakin kamshi suke a ido kawai kasan zasu yi dad'i, kowanne saida ta zuba mata taci ta k'oshi suma suka ci har Haisam ma aka zuba mawa Jidderh ta kai mashi, bayan sallar Azahar aka fara zuwa barka haka ta waya ma anata kiran Fatun ana mata barka har su gwaggo ma sun k'ara yin waya harda Vedio call suka ga yaran kowa sai farinciki yake.
Da daddare bayan sallar isha gaba d'aya yan gidan harda Dad nan part d'in su Fatun suka zo lokacin tuni sunyi wanka tun da yamma Fatuu na sanye da doguwar rigar Atamfa haka yaran ma anshirya su cikin set na Overall ash sai hira ake kan su ana nishadi, anan falon nasu aka ci Abincin dare sai wuraren k'arfe goma sannan Mom tasa su Yasmeen suje su kwanta Saboda zuwa school da safe itama dasu Dad duk sukai ma su Fatuu saida safe ganin Jidderh bata tashi ba yasa Mom ce mata mi take jira ta tashi su tafe sai Allah ya kaimu kuma a dasa zaman jegon cikin yar shagwaba tace ita anan zata kwana, wani kallo Mom tayi mata tace to shi Habibyn ya kwana a ina da sauri tace ba ga part d'in shi can sama ba ita kuma sai ta kwana ta taya Fatuu raino Mom tace to bazata kwana ba in don raino ne shi ya tayata,
"wayyo Mom don Allah ki barni in kwana wllh banson in yi nisa da y'ay'ana, kuma ai da ana da cikin su nima ba a dakina take kwana ba to nima yanzu zan rama ma k'ura aniyarta ne" dariya Mom tayi tace wannan kuma ai ita tasa kanta ko, dole Mom tasata ta mik'e tace daga baya ta kwana amman yau ta k'yale su suyi rainon babies d'in su da kan su tana tura baki ta bita bayan sunyi masu saida safe, babba babba ne wato da alama Mom ta fahimci Haisam d'in na buk'atar ke6ewa da matar shi ko kuma tasan zai so hakan don tun bayan da aka sallamo ta d'akin bai kasance ba mutane ba, bayan fitar su Mom bin juna sukai da kallo suna murmushi ita dashi yana zaune akan side drawer jikin shi sanye da farin voile, mik'ewa yay ya nufi gadon ya zauna daga baki gefen Fatun still da murmushi akan fuskokin su cikin cool voice d'in shi ya furta "Mai jego" dariya Fatun tay kafin tace "Na'am Angon jego" shima dariyar yayi ya maida idanun shi kan jariran dake a nad'e suna bacci asaman gadon itama kai idonta tayi kan su suka cigaba da kallon su a tare kowa dad'i ya cika mashi ranshi can Haisam d'in yay sigh ya furta "I'm forever grateful ya Rabbi" yana rufe baki Fatuu ta furta "We're forever grateful our perfect Rabb" jinjina mata kai kafin ya k'arasa hayewa saman gadon ya kai hannu ya jawota jikinshi ya d'aura habarshi a saman kanta sukai shiru suna ta sakin k'ayataccen murmushi, a hankali taji ya tambayi ya jikinta ta bashi amsa da ba abunda ke mata ciwo ya d'aga kai, shiru sukai kowa yana jin sabon son dan'uwan shi na ratsa zuciyoyin su can ta d'aga kai ta kalle shi ta tambayi yaushe Aunty Fanan zata zo ya bata amsa da jibi ta jinjina kai, kasa janye idonta tayi suka zuba ma juna ido breathing dinsu na had'uwa, sun d'an d'auki lokaci a haka can ta hura mashi iska a ido ya d'an kikkafta idanun ta saki dariya shima yar dariyar yayi ya k'ara matseta a jikin shi tare da furta "I Love You Baby, I don't even know how to tell you how much I love you" d'aga ido tay ta kalle shi tare da kashe mashi ido d'aya cikin wani irin salo ta furta "I can't get enough of Your love Hubby" tana rufe baki kawai sai gani tay ya had'e lips d'in su, da alama dai Fatuu har ta manta da nakudar da tayi shiyasa ta biye mashi, sun d'an d'auki lokaci a haka kukan jaririn daya karad'e d'akin ne ya dawo dasu hayyacin su da sauri suka saki juna suna dariya Fatun nata fad'in yanzu fa bashi kad'ai keda lokacin ta ba ya k'ara fad'ad'a dariyar tashi, Adam ne ya farka yana kukan tare da kai hannu baki yana tsotsa alamar yunwa yake ji, daukko shi tay ta shiga kiciniyar feeding nashi ganin haka yasa Haisam cewa ko ya taimaka mata tace eh ya kai hannu ya ruk'e mata shi, nursing pillow dake a ajiye gefe da d'azun tayi amfani dashi ta d'auko har ta iya yadda Aunty ta nuna mata bayan ta daidaita shi ta fara feeding d'in nashi sosae ya kama yana sha Haisam yay k'uri yana kallon shi can ya kalli Fatuu da alamun mamaki yace k'arami dashi yana shan abu haka ta saka dariya ta shiga bashi labarin yadda tun a Asibiti ya fara sha da tsiyar da Aunty tayi mashi, yana cikin sha d'ayan ma ya farka yana kuka Haisam ya tambayeta shima ko yunwa yake ji tace k'ilan yace to yanzu ya za'ai ga wannan na sha yadda yay Maganar har saida ya bata dariya tace ya d'auke shi wannan ya gama yace Ok ya k'arasa hayewa gadon ya d'aukko shi, yana d'aukar shi yayi shiru ya shiga mamular hannu idanunshi ya bud'e su sosae yana kallon Fuskar Haisam da shima kallon shi yake yana mashi murmushi, saida Adam d'in ya gama suka yi musaya ta amshi Aliyun, ganin yadda shima yake sha sosae yasa Haisam d'in ce mata anya zata iya shayar dasu duka kuwa, tana dariya tace mi zai hana ba ita ta haife su ba yace to amman in suna sha haka ai zata rame sosae tace a'a indai tana ci tana k'oshi lafiya lou, shima saida ya k'oshi sannan ta cire shi bayan ta goge mashi bakin shi da d'an towel mai taushi ta fara kokarin canza masu diaper d'in jikinsu kamar yadda Aunty tace kar ta bari su kwana dasu, koda ta cire basuyi komai ba dama ruwan zamzam ake basu amman duk da haka saida ta canza komai da zata buk'ata na daga gefenta cikin dresser dinsu mai kyau, bayan duk ta canza masu ta feshe su da turaren su ta maida komai, ganin ta kwantar dasu a kan gadon yasa Haisam ce mata ba ga gadonsu nan ba tace tunda dare ne gara ta kwantar dasu nan koda zasu tashi da daddare yace Ok, gaba d'aya bin yaran sukai da kallo suna masu murmushi su kuma duk sun k'ura masu ido sai kace sun san su waye su abun gwanin sha'awa, sun d'an d'auki lokaci a haka kafin Haisam ya kalleta yace yasan bata rasa jin yunwa ko tace a'a bata jin wata yunwa ai taci Abinci sosae da daddaren nan kawai tea take so zata had'a tunda ga kayan nan yace Ok bari ya had'a mata ya tashi tana ta kallon shi da murmushi ta furta "You're the best husband ever" k'ayataccen murmushi ya saki tare da furta mata thanks, tea mai k'auri ya had'o mata da kanshi ya rink'a bata tana sha bayan ta gama shima ta matsa mashi saida ya had'a duk da yace mata a k'oshe yake, bayan sun gama ya tambayeta akwae abunda zai taimaka mata yana son yay wanka tace a'a yaje yayi kaya kawai zata canza, a tunaninta a nan zai wankan sai taga ya nufi k'opa yace mata bari yaje sama yayi sai ya dawo tace to, bayan fitar shi mik'ewa tayi har zata tafi ta tuna wani abu ta koma kan gadon, Addu'oi ta shiga yi masu tana tofa masu Adam har ya koma bacci sai Aliyu ne idon shi biyu tana murmushi tace mashi Mom zata je tayi shirin kwanciya ta dawo sai kace yana gane abunda ta fad'a yay mata k'uri da ido, wurin kayanta ta nufa ta fara cire kayan jikinta bayan ta gama ta d'aura towel saida ta dauki pad da pant da zata canza sannan ta nufi toilet bayan ta yafa gyale a saman kanta, bata jima sosae ba ta fito ta koma wurin kayanta, shiryawa tay cikin bakar nursing nightgown ta d'aura brown robe a sama ta saka hula akanta bayan ta gama shiryawa ta nufi gaban mirror kallon kanta ta shiga yi tana fesa turare a cikin ranta take raya wai yanzu nan ita mai jego ce tana ta murmushi har ta gama ta juya ta nufi gado shima d'ayan har ya koma baccin, hayewa tay taja duvet ta lullube su tare da kai hannu ta rungumosu su duka, bayan wasu mintuna sai gashi ya dawo shima yayi shirin kwanciya sai zuba k'amshi yake, saida ya rufe k'opar d'akin sannan ya nufi gadon ta d'ago tana kallon shi ya kunna lamp kafin ya nufi switch ya kashe hasken d'akin sannan ya nufi gadon, ta d'ayan bangaren ya hau ya fara yin Addu'a bayan ya gama ya d'an tufa bangaren su Fatun da jikinshi sannan ya kwanta yana facing Fatun ta d'an hasken da ke akwai ya hangota tana mashi murmushi shima ya fara yi mata daga baya bacci ya kwashe su.
Washe gari talata bayan la'asar Hajiya ta iso, Haisam ne yaje ya d'aukko ta a Airport, bayan sun iso gidan gaba d'aya duk suna a part d'in mai jego Hajiya ta nufi can shi kuma Haisam ya nufi part d'inta don ya kai mata kayanta, suna zaune a falo harda mai jego har sunyi wankan yamma tana sanye da half gown ta sabuwar atamfa golden tayi yar kwalliyarta ta fito fess haka yaran ma duk anyi masu wanka an saka masu kaya iri daya light blue abun saidai ace Masha Allah d'aya na hannun k'awar Mom da tazo barka d'ayan kuma na a hannun d'iyarta wadda k'awar Jidderh ce dama tun d'azun aketa zuwa barka harda Abokan Dad ba'a ma dad'e da maido yaran ba daga part d'in Dad d'in harda kyautar kud'i aka yi masu, Hajiya na yin sallama gaba d'aya su twins dasu Yasmeen suka nufota da gudu suna fad'in "Oyoyo Granny" duk suka k'ank'ame ta Jidderh ma ta taso ta nufota tana mata Oyoyo, Hajiyar na dariya tace ma su Twins sai sun karyata tun bata ga sabon angon nata ba salon yace bai sonta duk suka d'ago suna dariya tace su shiga ciki, mik'ewa Mom da Aunty sukai suna mata sannu da zuwa tana amsawa ta nufi kujera ta zauna su twins d'in ma duk suka zauna a kusa da ita sun shishshige mata, zama su Aunty sukai suka shiga gaishe da ita tare da yi mata an zo lafiya K'awar Aunty ma ta gaishe da ita tare da yi mata anzo lafiya haka d'iyarta ma, Mom ce ta amso Babyn hannun Friend d'in tata ta kawo ma Hajiya Jidderh kuma ta amso na hannun d'iyar matar k'awarta ta zo gefen Hajiya dashi tana nuna mata, bin su da kallo Hajiya tay fuskarta d'auke da fara'a ta shiga fad'in Ma sha Allah, mik'ewa K'awar Mom tayi tay masu sallama tare da yi ma Hajiya barka suka tafi Mom ta rakasu, juyawa Hajiya tayi ta kalli Fatuu dake d'an murmushi tace "Sannu da kokari Fateema, sannu kin dai yi aiki ba kad'an ba wllh yara haka Tubarkallah, to Allah ubangiji ya raya mana ya Albarkaci rayuwar su kema ya k'ara maki lafiyar shayarwa" gaba d'aya harda su twins suka had'a baki wurin amsawa da Amin,
"To ni bansan wanene sabon Angon ba bansan waye kuma d'an ba a cikin su a bambance man" Hajiya ta fad'a da fara'a, gaba d'aya su Jidderh suka zuba masu ido suna kokarin bambanta mata saidai duk sun kasa Saboda duk bacci jariran ke yi balle su bambance su ta ido sai faman canki canka suke abun ma sai ya zama abun nishad'i Aunty nata dariya don ita tasan kowanne Saboda tare da Mom suka kaisu wurin Dad haka lokacin da za'a maido su ita Dad ya kira taje ta amso su tare da Yasmeen lokacin Jidderh bata a d'akin tun lokacin ta ruk'e Adam aka ba k'awar Mom sai d'iyarta aka bata Aliyun, ita kanta Yasmeen da suka amso su tare duk ta rud'e ta kasa bambanta su, Hajiya sai faman dariya take tana fad'in lalle ashe aiki ne tantance su, Haisam ne ya shigo Hajiya ta d'aga kai ta kalle shi tace "to kai Baban su sai kazo ka bambanta man su tunda duk sun kasa" murmushi yay kawai ya nemi kujera ya zauna tace ya zai zauna ko shima bazai iya banbance su bane ya d'aga mata kai alamar eh kafin cikin cool voice d'in shi yace duk suna bacci dama ta ido ake gane su, jinjina kai Hajiya tayi tace shima kenan sai ta idon zai iya gane su ya d'aga mata kai,
Aunty dake ta dariya tace to a tambayi Mom d'in su k'ilan ita ta gane su duk aka maida kallon kan Fatuu dake murmushi Hajiya tace tazo ta bambance mata su, mik'ewa tay ta matsa kusa dasu ta d'an sunkuya tana kallonsu, ta d'an d'auki lokaci kafin ta d'aga yatsa ta nuna na hannun Hajiya tace shine Hajiyar ta tambayi shine wa tana yar dariya tace Angonta,
"To wa zai tabbatar mana in daidai ta canka" Hajiya ta tambaya tana dariya Aunty tace daidai ta canka shine Hassan d'in don ta ruk'e tunda suka kaisu wurin Dad, da sauri Jidderh tace "Sis Fatuu ya akai kike gane su don Allah?" gaba d'aya akai dariya Hajiya tace tunda koda yaushe tana tare dasu tana k'are masu kallo dama zata iya samun abunda zata rink'a banbance su, duk su Yasmeen suka hau rok'on ta nuna masu yadda suma zasu rink'a gane su, nuna masu girar Adam d'in tayi tace tanan ta gane shi don zanen tashi ya d'an fi lankwasawa kad'an aikuwa duk suka maida idanun nasu kan su harda Hajiya Aunty ma ta taso daga kujerar ta tazo don ta gani sai gashi sun ga hakanne amman sai mutum ya natsu sosae zai gane, Mom ce ta dawo d'akin tana d'auke da madaidaicin tray an d'auro ruwa da lemu da glass cup Dad na biye da ita, ganin suna ta dariya yasa ta tambayi ya akai Aunty ta bata labari Dad yay dariya yace shima in dai ba idon su biyu ba bazai gane ba, zama yay kan kujera ya d'an sunkuyar da kai ya gaishe da Hajiya tare da yi mata anzo lafiya bayan ta amsa yace bai gidanne sun fita tare da bak'i tace ba komai sai kuma tayi mashi barka, saman c-table Mom ta d'aura tray din tace ma Hajiya a kawo Abinci anan ne tace mata a'a bata jin yunwa yanzu, hira suka shiga yi cike da nishad'i ana haka jariran suka farka daga bacci nan suka k'ara tantance su ta idon su, sai da akayi sallar Magrib sannan duk suka tashi don zuwa yin salla.
Washe gari wuraren k'arfe sha biyu na rana Fanan ta iso tare da Nameer suma Haisam ne yaje ya d'aukko su daga Airport tana sanye cikin brown coat dress tasa yar bak'ar himar sosae tayi kyau Nameer ma na sanye da k'ananun kaya jeans da t-shirt, gaba d'aya Fanan a k'agare take da taga jariran da suna hanyar zuwa gidan sai faman zumud'i take tana ma Haisam tambayoyi game dasu Nameer nata mata dariya, lokacin da suka isa ma'aikatan gidanne suka zo suka d'auki kayan su tare da yi masu sannu da zuwa suka nufi ciki, ba kowa parlon Fanan ta tambayi Haisam inda Fatun take ya nuna mata ta nufi part d'in da sauri shi kuma Haisam da Nameer suka tsaya don ganin an shiga da kayan nasu, lokacin da ta shiga parlon ba kowa hakan yasa ta nufi Bedroom d'in, Mom da Aunty sai Hajiya ne a ciki yaran gidan duk suna Makaranta Fatuu na a zaune tsakiyar gado tana sanye da doguwar rigar shadda tayi daurin kallabi mai kyau haka yaran ma suna sanye da fararen kaya suna bacci daga gefenta, da Sallama ta shiga duk suka kai idanun su kanta ta shiga ganin itace yasa gaba d'aya suka shiga yin murmushi harda Fatuu ta nufi gadon da sauri ta zauna a baki idonta akan yaran ta shiga sakin faffad'an Murmushin dad'i harda d'an yarfa hannu, saida ta gama kallon su sannan ta juyo tana gaishe dasu Mom Hajiya tace wato saboda zumud'in ganin yaranta sai yanzu zatai lokacin su tana yar dariya tace a'a, anzo lafiya suka yi mata ta amsa kafin duk suka yi mata barka tana ta washe baki idonta akan yaran take amsawa Fatuu ma ta gaishe da ita ta kalleta bayan ta amsa tace "Sannu sis, sannu da k'ok'ari don Allah. Look at them, very cute wllh" dariya kawai Fatun ke yi haka su Mom don gaba d'aya ta rud'e da ganin yaran, su Haisam ne suka shigo Nameer ya nufi gefen Hajiya ya zauna tare da gaishe da ita ta dafa Shoulder d'inshi tana mashi an zo lafiya bayan ya amsa ya gaishe dasu Mom suma duk suka yi mashi anzo lafiya, Hajiya ce tace mashi shi bai ga yaran nashi ba ya juya yana kallon su fuskar shi d'auke da Murmushi yace "Ma sha Allah, Allah ya raya mana su" gaba d'aya aka amsa da Amin, ganin yadda Fanan ta tsura masu ido yasa Hajiya tace to ta d'auke su mana da sauri tace "No, suna hutawa a k'yale su suyi baccin su in sun tashi na d'auke su suga Mom d'in su" Hajiyar tace to mai y'ay'a duk akai dariya, shiru Fatuu tay kamar mai tunanin wani abu idonta akan Fanan dake ta kallon yaran tana murmushi can ta kai hannu ta d'aukko Aliyu wato Hussein dake a kusa da ita hakan yasa Fanan kallonta kawai sai gani tay ta Mik'o mata shi tana d'an murmushi, kallon rashin fahimta ta bita da shi haka ma su Hajiya duk idanun su na akan su,
"Aunty Fanan gashi, na baki shi ",
da k'yar ta furta Maganar, d'an yamutsa fuska Fanan tay cikin d'aurewar kai