Showing 474001 words to 477000 words out of 512766 words
Chapter 159 - Asanadin Makwabtaka Book 3 Hausa Novel Complete
Unknown
27 Dec 2024
1576
ne tunda akwae cctv yace ta bari in suka kusa isa sai ta hau taxi ɗin, tun a cikin Motar ta naɗa gyalenta tayi kamar niƙab a cikin Motar suka yi bankwana da Dad ɗin nata duk ya damu, bayan ta fito saida ta samu taxi ta hau sannan Dad ɗin nata ya tafi har suka isa Airport bata buɗe fuskarta ba sai bayan data shiga tana janye da trolley da zasu tafi sannan ta buɗe, bayan sun iso Kano fuskarta a rufe ta bar Airport ɗin ta hau keke napep don ya kaita tasha, wuraren azahar ta iso Katsina ta kira Hajiya ta sanar mata ta tambayi inda take bayan ta faɗi mata ta kira Tk ta sanar dashi ya ɗauki Mota tinted yaje ya taho da Farhar tace kada ya ɗaukkota a tashar in ya kusa isa ya kirata ta fito sai su haɗu kan hanya ya ɗaukkota, duk yadda Hajiya ta tsara haka akayi lokacin da suka iso gidan Hajiya na Bedroom bata daɗe da gama yin sallar Azahar ba Farhar ta shigo tana hangota ta nufota da sauri tana zuwa ta faɗa jikinta tana kuka Hajiyar na murmushi tace mata ya isa miye abun kuka, gaba ɗaya su Saude da Husnah harda Tk saida Hajiya taja kunnansu kan kar wanda ya sake ya bayyana Farhar na gidan koda za'a tambaye su nan gaba har su Gwaggo tace kar a bari su san da zuwanta gidan duk suka ce to, itama Farhar tace mata kada ta bari kowa yasan tana gidan har Kamalun tace to. Lokacin da Dr ya kira Hajiya Maryam da alamun tashin hankali ya sanar mata zancen barin Farha gida da takardar data bari harda wayarta zo kaga rawar jiki da tsananin tashin hankali ta shiga tambayar ina taje ya akai har ta bar gida ba wanda ya sani yace to shi dai ya tafi wurin aiki yara kuma an tafi kai su School koda ya dawo dubata kamar yadda yake yi sai dai takarda ya gani kuma ya tambayi security sun tabbatar mashi da fita tayi kuma cewa tayi wurinta zata zo Abuja, a fusace tace to ubanwa yace su bari ta fita Dr yace sunce ba'a basu umarnin su hana wani ya fita ba sai lokacin ta tuna da haka gaba ɗaya ta gama ruɗewa tace mashi a bibbincika inda ake tunanin zata iya zuwa pls yace mata bai tunanin zata tsaya kusa don da gani ta shirya ma abun bazata tsaya inda za'a ganota ba shi dama abunda yaketa kwatanta mata kenan tace yanzu ba lokacin wannan bane duk da haka adai bincika ko ina itama zata kira wasu wuraren taji ko taje can, abu kamar wasa har zuwa yamma ba'a ji taje wani wuri ba, lokacin da ta kira Hajiya ta tambayi ko Farha tazo da alamun mamaki ta tambayi ina Farhar taje farko shiru Hajiya Maryam ɗin tayi saida Hajiya ta ɗaga mata murya tace bazata faɗi mata ba sannan tace aje takarda tayi wai tunda baza'a bata wanda take so ba ta shiga duniya, wani salati da Hajiya ta saka baka ta6a cewa tasan inda Farhar take da alamun tashin hankali tace yanzu duk Maganar data yi mata shine bata ji ba saida tayi sanadin barin ta gida kamar Hajiya Maryam ɗin zatai kuka tace yanzu dai don Allah ta bar Maganar a taya su bincikawa inda ake tunanin zata iya zuwa, zuwa dare har zancen 6atan Farhar ya fara baza wurare har Mai girma shugaban ƙasa yaji sosae hankalinshi ya tashi ba kamar da yaji cewa takarda ta aje ta tafi shima da kan shi ya shiga kiran yan'uwa na jiki yana tambayar ko taje in aka ce bata je ba sai yace to a taya su bincikawa, lokacin da ya kira Hajiya nan ta warware mashi komai tace su kwantar da hankalinsu Farhar na wurinta amman kada a bari Hajiya Maryam ɗin taji in ba haka aka yi mata ba bazata saduda ta ƙyale yarinyar ba hakan kuma na iya haifar da abunda za'ayi dana sani tunda yaran zamani ba'a cewa za'a yi masu dole yace ya fahimta, Washe gari tunda safe Hajiya Maryam ta koma Lagos nan fa aka hau bincike wurare daban daban har gidajen radio da Tv aka kai cigiya ko wani ya ganta har binciken lambar wayarta akayi aka tabbatar wayar da tayi ta ƙarshe anan Lagos ne, kan kace mi zancen 6atan ya karaɗe social media ana ta faɗin ɗiyar ƙanwar shugaban ƙasa kuma Minister Maryam Adamu Zakee ta 6ace sai dai ba wanda yasan dalilin 6atan nata don ba'a bayyana ba da yawan mutane sun tafi akan ƙilan kidnapping ɗinta akai, har su Fanan sun samu labarin sosae hankalin Fanan ya tashi har ta fara shirin tahowa Nigeria Haisam ya kira Hajiya kan 6acewar Farha ɗin nan ta bayyana mashi komai tace su kwantar da hankalinsu amman kada wanda ya sanar ma Hajiya Maryam ɗin saida Fanan taji haka sannan hankalinta ya kwanta har waya sukai da Farhar amman ita Hajiya Maryam duk sai suka nuna mata hankulansu ya tashi, da yake abun na masu ƙasa ne an zurfafa bincike sai gashi zuwa yamma an tabbatar da ta siya ticket online kuma ta hau jirgin Kano a jiya nan da nan bincike ya koma Kano, bayan an tabbatar da taje kano Hajiya Maryam ta kira Hajiya ta sanar mata ta tambayi ko ta ƙaraso nan Katsina Hajiya tace a'a bata zo ba ai in nan zata zo mi zai sa ta hau jirgin Kano, cike da nuna Al'ajabi Hajiyar tace "to amman wai mi zaisa Farha taje kano, ko kinada mutanen da kike tunanin zata iya zuwa can wurinsu??" cike da damuwa Hajiya Maryam tace tana da abokan kasuwancinta acan saidai Farhar bata san su ba sai kuma abokanta da sukayi karatu tare suma ba kowanne Farha ta sani ba sai wata ƙawarta guda Hajiya Turai kuma ta kirata ta tambayi ko Farhar taje wurinta ta tabbatar mata da bata je ba,
"Oh ya Allah, shiyasa aka ce maganin kada ayi to kada a fara yanzu ina amfanin haka ace budurwa kamar Farha ta 6ace ai dole a shiga dumuwa da tashin hankalin halin da take ciki, yanzu da ta tafi Kano mi taje yi can in ma acan ɗin ta tsaya, to ko dai yin Film ta tafi ne don naji ance dama wasu yan wasan hausan sanadin auren dole suke tafiyar su su shiga, to in ma dai Film ɗin taje yi ai da sauƙi don tana farawa za'a ganta tsorona ace ba a Kanon ta tsaya ba ta haɗu da wata yar Kano to Jidda ta hure mata kunne kan ta gudo wurinta ta fitar da ita waje....." da sauri Hajiya Maryam ta katseta da faɗin "Don Allah Hajjaju ki daina yin wannan fatan",
"To Maryam na bari Hankalina ne ya tashi na rasa tunanin da zanyi kan inda ta dosa amman in sha Allahu tana a hannu nagari Allah zai tsareta" da sauri Hajiya Maryam ta amsa da Allah yasa kafin a zuciye tace "In dai ba'a ganta ba zuwa gobe ina nan zuwa Katsina zan sa a kama yaron nan da kaf danginshi a tuhume su na tabbatar basu rasa sanin inda take don haka sai sun nemo man yarinyata",
da sauri Hajiya tace "akan me, ke waya faɗi maki su suka ɗauketa, yarinyar da daga gani ita ta shirya ma kanta hakan tunda har da takarda ta aje to ina ruwan yaro da dangin shi anan?" a fusace tace ai zai iya yuwuwa shiya tsara mata,
"Ba wani tsara matan da yayi yaron da tun farko ita ta bayyana mashi so nan fa Kakarshi tazo cikin damuwa kan bata son al'amarin gudun matsala sai kuma suja ma kan su matsalar, don haka ni ban amince kisa ayi masu wani abu ba don na tabbatar basu da sa hannu a 6atan ta in kuma kika ƙi jin maganata kika sa akai ma yaron mutane wani abun ita mai guduwar ta samu labari al'amarin ya ƙara kwa6ewa to ba ruwana kar ma kice zaki kirani dama yanzu ai harda ƙin jin maganata yasa hakan ta faru don haka na dai gaya maki ban amince kisa ayi masu wani abu ba muci gaba da Addu'ar bayyanarta da kasancewarta cikin ƙoshin lafiya" a sanyaye ta amsa mata da Amin kafin sukai sallama, bincike ya tsananta a Kano a gidajen radio da tv da social Media harda Airport anata cigiya harda hotunan Farhar da ranar data zo kano harda kayan jikinta, duk abun nan su Gwaggo basu sani ba kawai dai Kamalu nata kiran layinta bai shiga har ya fara shiga damuwa dama lokacin da tana gida cikin halin damuwa sunyi waya har yake mata magana kan jin muryarta ta canza tace mashi bata jin daɗi ne duk sai tunanin shi ya tafi akan ko ciwon ne yay tsanani yasa ba'a samunta a waya, sai ranar juma'a lokacin kwana ukku da 6acewarta Kamalu yaje School wani abokin shi da suke tare ya nuna mashi hoton Farhar a Facebook yace mashi wai wannan ba itace wannan ɗiyar Minister ɗin ba ƙawarshi da yake ganin hotunanta a wayarshi da sauri Kamalun yace mashi eh itace miya faru nan yake ce mashi wai nemanta ake ta 6ace ai da sauri ya warci wayar yana dubawa nan ya tabbatar da hakan yana bashi wayar ya miƙe sai gida, Lokacin daya dawo a falon Gwaggo ya isketa tare da Amadu da Haulat duk sunyi jugum tun bayan da Amadu ya shigo masu da labarin 6atan Farhar suke haka kowa ya kasa yin ƙwaƙƙwaran motsi, shima zama yay cikin tashin hankali yace masu ko sun samu labarin daya samu yanzu a School wai Farha ta 6ace duk suka ɗaga mashi kai ai shima sai ya nemi wuri ya zauna, bayan wani lokaci Gwaggo ta sauke nannauyar ajiyar zuciya cike da damuwa tace ita dai fatan ta Allah yasa ba dalilin abunda tazo dashi bane tunda dama tace ma Kamalu ita tasan yadda zata sa iyayenta su amince in ko har hakan ne to kuwa akwae babbar matsala, jin Maganar Gwaggo yasa cikin Kamalu juyawa Amadu yace mashi suna waya da ita ne nan ya faɗi masu rabon shi da ita a waya Haulat tace Allah yasa dai ba dalilin hakan yasa ta 6ace ba Allah kuma yasa a ganta duk suka amsa da Amin, Amadu ne yace bari ya kira Fatuu yasan ta bakinta zasu iya jin dalilin 6acewar tata, bayan ta kira sun gaisa yake mata zancen Farhar yace da gaske wai ta 6ace tace mashi eh ya tambayi tasan dalilin 6acewar tata nan ta faɗi mashi guduwa tayi don harda takarda ta aje Mom ɗin su taƙi yarda da Kamalu shine ta yanke yi mata auren dole da Cousin ɗinta da suke yin soyayya a satin data gudun, salati Gwaggo ta saka tare da rufe ido ta dafe goshi shi kuwa Kamalu zumbur ya miƙe yay hanyar ɗakin shi yana zuwa sai toilet, Fatun bata fito ta bayyana masu inda Farhar take ba duk da ta sani saboda Hajiya tace kar a faɗi ma kowa sai dai ta shiga kwantar masu da hankali tace in sha Allahu za'a ganta tunda har an gano ta hau jirgi taje kano Amadu yace to Allah yasa ta amsa tace ina Gwaggo yace gata nan tayi jugum duk tsoro ya kamata tace Kamalu fa yana yar dariya yace shi wannan yana tunanin yana toilet don yana jin bayanin data yi ya miƙe yay hanyar ɗaki Fatun tay yar dariya tace su kwantar da hankalinsu tasa aka ba Gwaggo suka gaisa nan ta shiga kwantar mata da hankali ita dae sai uhmm da to kawai take cewa, suna gama yin wayar Gwaggo ta miƙe tace bari taje tayi ma Hajiya jaje Haulat ma ta miƙe tace bari ta sako Hijab suje, lokacin da suka je Hajiyar na bedroom Farha kuma tana a ɗayan bedroom ɗin Husnah tanata shan bacci abunta dama nan Hajiya tasa ta zauna gudun kada Momynta tayi zuwan bazata, Saude ce ta kirawo masu Hajiyar bayan ta shigo cikin falon tana ɗan murmushi tayi masu sannu da zuwa tare da yi masu barka da Juma'a duk suka amsa suka gaisheta, Gwaggo ce ta fara mata jajen tace su wllh basu san abunda ke faruwa ba sai yau da su Amadu suka ga ana cigiyarta a waya Hajiya na ɗan murmushi tace tsakaninta ne da uwarta taƙi goyon bayan wanda take so ƙarshe ma sai ta yanke yi mata auren dole to dama yaran zamani ana masu dole ne shine ta kaɗa kai tayi gaba abunta, cike da damuwa Gwaggo tace wllh tun farko irin haka take ta gudu don tasan abu ne mai wuya iyayenta su amince Hajiya tace shi mahaifinta ma ya amince uwarce taƙi da yake taurin kai ne da ita sai kuma ta samu yarinya irinta sai suyi ta cakusawa, itama Haulat jajen tayi mata da Addu'ar Allah ya bayyanata ta amsa da Amin ganin yadda Gwaggo tayi gwalau duk ta shiga damuwa yasa Hajiyar yin yar dariya tace "Amaryar Mani ya ya, ko kina tsoron hukuncin da Minister zata yi maku na kun yi silar 6acewar ɗiyarta" ɗan motsa baki Gwaggon tayi kafin tace a'a kawai dai 6acewar mutum bata da daɗi ba'a san a wane hali take ciki ba, Hajiyar tace mata kar su damu za'a ganta ne suka ce Allah ya sa, bayan sun mata sallama sun fito ne Haulat tace ma Gwaggo ita sai taga kamar Hajiya tasan inda Farhar take don taga kamar bata damu ba Gwaggo tace itama ta lura ƙilan kuma kawai ƙarfin zuciya ne Haulat ɗin ta ƙara cewa ko kuma shiri ne akai don Hajiya Maryam ɗin ta saduda Gwaggo tayi shiru tana nazarin Maganar, har aka shiga Weekend shiru Farha bata bayyana ba Kamalu kuwa yana can yana zazza6in zullumi, ranar Lahadi Dr mijin Hajiya Maryam ya kira Hajiya anan yake sanar mata ba ƙaramin tashi hankalin Hajiya Maryam yayi ba ko isasshshen bacci bata yi taita kuka tana faɗin tayi sanadin 6acewar ɗiyarta waya sani ma ko ta mutu shi yanzu tausayi take bashi sosae gashi sai zuba kuɗi take ana cigiya a gidajen tv da radio yanzu har kuɗi tasa masu yawa na duk wanda ya kawo ta ko ya faɗi inda take zata bashi, murmushi Hajiya tayi tare da ɗan ta6e baki tace mashi ya ƙyaleta ta ɗan ƙara jin jiki tukun su kuma kuɗi da take 6atarwa na cigiya ai tana dasu ne don haka suma kafafen sadarwar ta fitar masu da zakka Dr ya ɗan yi shiru kafin yace shi abunda yake gudu kada wani ciwon kuma ya haye mata Hajiyar tay murmushi mai ɗan sauti jin yanzu kuma ta matar shi yake tace mashi kada ya damu ba ciwon da zai haye mata in ba hakan aka yi mata ba bazata daina taurin kai ba, bayan sun gama yin wayar shiru Hajiya tayi ta ɗan ta6e baki a ranta ta shiga raya in ba don ta kama ba ita kanta ai bazata so ta tada ma ɗiyarta hankali ba, damuwa tasa Hajiya Maryam ƙin komawa Abuja har wata rama tayi daka ganta kasan tana cikin damuwa bayan Hajiya ta warware ma President komai ya kira Hajiya Maryam ɗin sosae yayi mata faɗa yace al'amarin irin wannan ai a hankali ake bi da ta saurari Hajiya duk da hakan bata faru ba yakamata ta daina saurin fushi ta rinƙa bin komai a hankali tana ƙwalla tace mashi in sha Allahu zata rinƙa bin komai a hankali su Mom ma duk sun kirata sunyi mata jaje har suna cewa zasu zo Lagos ɗin suyi mata jaje tace ba sai sun zo ba kawai dai don Allah a tayasu bincikawa ba kamar wurin mutanensu dake Kano suka ce dama duk sunsa anata cigitawa in sha Allahu za'a ganta, Fanan ma ce mata tayi tana son tazo Nigeria ɗin amman ta ɗan ƙara saurarawa ne ko Farhar zata taho wurinta daga Kanon Hajiya Maryam ɗin tace hakan yayi kada ta taho, a ranar Monday da daddare Hajiya ta kira Hajiya Maryam tace mata gobe tazo tana son ganinta tana jin haka da sauri tace mata ko Farhar tazo wurinta ne tace mata a'a tana son yin magana da ita ne...........
103
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
........Washe gari da safe jirgin su ya sauka tare da security detail ɗinta aka ɗaukkosu zuwa gidan Hajiya motocin escort gaba da baya sai Jeep ɗin da take ciki a tsakiya, koda Hajiya ta ganta saida ta jinjina yadda ta rame, a bedroom ɗinta suka zauna tana kallonta tace ashe ta damu da Farha har haka amman shine taƙi goyon bayan abunda take so Hajiya Maryam ɗin ta ɗan yamutsa fuska kafin cikin karyayyar murya tace ai dole ta damu ace yarinyarka budurwa tabar gida ita damuwarta a wane hali take ciki ina taje, tana yin Maganar ƙwalla suka zubo mata sharr Hajiya tace "in sha Allahu tana cikin ƙoshin lafiya kuma a hannu nagari" a hankali ta amsa da Allah yasa,
"Yanzu in aka ganta zaki goyi bayan abunda take so ko?" Hajiya ta tambaya tana kallonta tay ɗan jimm kafin tace "Hajjaju ni a ganina ba kowanne abu yaro ke zuwa dashi a goya mashi baya ba, komai da nike yi saboda rayuwarta ta inganta ne taya za'a ce Farha ta auri yaro kamar wannan bacin ga wanda ya gina rayuwarshi wanda zai ruƙeta da kyau muna gani sai mu barta taje ta jefa rayuwarta a wahala"
ɗan murmushi Hajiya tayi tace "idan abunda yaron yazo dashi baida wani aibu lafiya lou sai a goya mashi baya mana, sannan Maganar gina rayuwa ai shima baki san abunda Allah zai yi ma tashi rayuwar ba tunda yanzu yake kan gina ta, sannan Maganar jefa rayuwa a wahala shi wanda kike hangen zai ruƙeta da kyau saboda kuɗi ke a tunaninki mai kuɗi ne ke ruƙe mata da kyau, Matan masu kuɗi nawa ne suke cikin damuwa a gidajen auransu har suna ganin dama talaka suka aura wanda zai basu farinciki, ko kuwa