Showing 486001 words to 489000 words out of 512766 words
Chapter 163 - Asanadin Makwabtaka Book 3 Hausa Novel Complete
Unknown
27 Dec 2024
1597
girma shugaban ƙasa ya turo wakilci an zo anyi masu gaisuwa, duk a ranar dasu Mom suka zo suka koma amman su Fatuu sai da akayi sadakar uku washe gari suka dawo.
Ƙarshe dai kuɗin da Fatuu ke tarawa canza ra'ayi tayi tunda an kai Baffan nata makka ta yanke buɗe Foundation da zata fara tallafa ma talakawa a Katsina, koda Fanan taji niyyarta nan tace itama tana so su buɗe tare Haisam daya ji ya basu goyon baya harda gudunmawa, haka su Mom harda Hajiya Maryam da President duk suma sun basu gudunmawa, daga baya aka buɗe Foundation ɗin mai suna HAIFAT FOUNDATION, bayan buɗe shi a hannun Gwaggo suka damƙa kula da shi su kawu Amadu da Tk da matansu su Haulat da Husnah suka zama masu taimaka mata wurin gudanar da ayyukanshi harda Aunty Mareeya da Feenah duk sun shiga cikin masu gudanar da ayyukan shi sai fatan Allah ya sanya albarka,
Bayan komawar President Ali kan mulki da shekara ɗaya da wasu watanni ne Hajiya ta kwanta rashin lafiya, farko daga zazza6i ranar wata lahadi ta tashi da shi bayan tasha magani ta ji ta samu sauƙi, da daddare bayan ta kwanta ciwo ya dawo mata zuwa wayewar gari jikinta yayi zafi sosae lokacin da Tk ya dawo daga Masallaci ya je gaisheta kamar yadda yake yi kullum da ƙyar ta amsa mashi sallama, bayan ya shiga a kwance ya isketa saman carpet tana sanye da Hijab da ƙyar tayi ƙarfin hali tayi Salla, jin yadda ta amsa mashi gaisuwar tana nishi dama gashi ya ganta a kwance ƙasa yasa shi tambayarta kamar bata lafiya tace mashi tun jiya take jin zazza6i sama sama tasha magani to da daddare ya idasa rufeta yanzu ma da ƙyar tayi salla yana jin haka da alamun tashin hankali yace bari ya fiddo Mota su tafi asibiti, batare daya jira jin mi zata ce ba ya miƙe da sauri ya nufi ƙopar fita, bayan ya fito saida ya shiga yayi ma Husnah magana kan taje ta taimaka ma Hajiyar ta shirya sai su tafi asibitin tare, itama hankalinta ya ɗan tashi jin Hajiya ba lafiya don da wuya kaji ciwo ya kwantar da ita kaji dai tana cewa bata jin daɗi, bayan zuwan su Asibitin wanda suke zuwa ba 6ata lokaci aka dubata tare da yi mata aune aune bayan an turo result likita ya yi masu bayanin zazza6in malaria da typhoid ne ke damunta har saida Hajiya ta ɗan yi mamakin jin harda typhoid, da likitan yace ko a bata gado don a dubata sosae ta kuma huta tace a'a adai yi mata abunda ya dace yanzu ta koma gida sai taci gaban da shan magani, bayan anyi mata allura an bata maguguna suka tafi, sai bayan da suka dawo Saude tasan da rashin lafiyar nata nan fa suka shiga bata kulawa kowa ya damu Hajiya ba lafiya Tk yace ko ya kira Haisam ya sanar mashi Hajiyar tace a'a kada a tada masu hankali zata samu sauƙi in sha Allah, Amadu ne ya kira Tk kan ya fito su wuce wurin aiki yaga lokaci na niyyar ƙurewa ya sanar mashi da Hajiya ce ba lafiya, Gwaggo na jin Hajiya ba lafiya suka taho harda Haulat da Amadun, gaba ɗaya duk kowa ya shiga damuwa gashi bata cin abinci sai ɗan abu mai ruwa shima daga baya aman abunda tasha ta fara yi ganin haka yasa tk yace ko su koma asibitin tace mashi a'a dama haka zazza6i yake da naci ai zata samu sauki, wasa wasa saiga ciwo nata gaba maimakon a samu sauƙi cikin kwana biyu sai gashi ya kai komai sai su Saude sun yi mata lokacin da Gwaggo tazo taga halin da take ciki ta tambayi Tk yan Abuja sun san bata lafiyar cikin damuwa yace Hajiyar ta hana a sanar masu Gwaggon tace ai ba biye mata za'ai ba, nan take ta buga ma Haisam waya ta sanar dashi da alamun tashin hankali ya tambayi abunda ke damunta ganin ko jiya sunyi waya da ita amman bai gane bata lafiya ba tayi mashi bayani, ana gama sallar Magrib sai ga Haisam ɗin ya iso Tk ne yaje ya ɗaukko shi tun suna kan hanyar zuwa gidan Dad ɗin shi da Hajiya Maryam suka kira suna tambayar ya isa ya jikin Hajiyar yace masu yana hanyar zuwa gidan, lokacin da yaga yanayin jikin Hajiyar bayan ya iso hankalinshi ya ƙara tashi don duk ta faɗa da gani tana jin jiki Haisam ɗin yace ma Tk tun yashe ne bata lafiya cike da damuwa yace kwananta biyu nan ya sanar mashi yadda sukai da likita harda kwantar da itan da akace za'a yi taƙi, bayan Dad ɗinshi ya kirashi ya sanar mashi gaskiya tana ɗan jin jiki Hajiya Maryam harda Vedio call suka yi taga Hajiyar nan fa hankalinta ya ƙara tashi tace ma Haisam gobe da safe zata zo ta ɗauketa, a daren ranar mutanen da suka ji zancen ciwon duk da zullumi suka kwana, washe gari wurin ƙarfe bakwai Hajiya Maryam ta iso nan ta hau su Tk da faɗan ya tana rashin lafiya zasu ƙi kira su sanar tunda ta fara ciwon, bawan Allah harda yar ƙwallan shi yace mata Hajiyar ce ta hana don kada a tada masu hankali aikuwa ta ƙara balbale shi da faɗa harda cewa ko don ba Mahaifiyarshi bace, wannan kalma ta saka shi fashewa da kuka, cikin halin ciwo Hajiya tace mata don me zata faɗi mashi haka bata ji yace ita ta hana ba ko so take yay mata rashin biyayya yaƙi jin Maganarta ganin ran Hajiyar ya 6aci ga kuma halin da take ciki yasa ta ba Tk ɗin haƙuri kan Maganar da tayi, wuraren ƙarfe sha ɗaya suka tafi da Hajiyar Abuja aka bar su Tk da kewa da damuwa sai Addu'ar Allah ya tashi kafaɗun Hajiyar suke, su Gwaggo ma duk sun damu haka yan'unguwa da yawanci duk basu san da Hajiyar bata lafiya ba sai yau da aka tafi da ita duk an damu yara da manya anata mata Addu'o'i.
Bayan zuwa da Hajiya Abuja a babban private hospital ɗin likitansu na Germany wanda yana ɗaya daga cikin likitocin da Shugaban ƙasa ya maido nan wanda yana aiki a Asibitin Gwamnati sannan kuma ya buɗe private hospital ya zuba ƙwararrun ma'aikata wanda wasu abokan aikinshi ne a can, bayan anyi mata aune aune aka tabbatar da abunda akace yana damunta a Katsina suke damunta kuma ma da sauƙi sosae nan aka tabbatar da jikinta yana buƙatar hutu sosae wataƙil bata hutawa sosae ko tana yawan yin zurga zurga, ran Hajiya Maryam ne ya 6aci tace ita dama ba son zamanta take a Katsina ba kawai don ta nuna hakan take so tunda basu a kusa da ita dama ai abunda taga dama zatai tayi ba mai hanata ko aikin NGO da take da ƙyar aka samu ta daina, ita dai Hajiya jin abunda likitan yace kawai tayi don tasan ita ba wata zurga zurgar da take yi, a ɗaki na musamman aka kwantar da ita sosae ake bata kulawa hatta zuwa dubata an ware lokacin da za'a rinƙa zuwa don kada a dameta, bayan sati ɗaya sai gashi jikin nata ya fara yin kyau lokacin har massaging jikin ake mata ana kuma bata lafiyayyun abinci da zasu ƙara mata ƙarfi da kuzari, bayan tayi satin su Tk da Gwaggo suka zo dubata harda Amadu gaba ɗaya sunji daɗi ganin yadda ta fara samun sauƙi ba kamar Tk kullum da zullumin ciwon nata yake kwana duk ya damu kwanansu biyu suka koma, bayan sati biyu aka sallameta suka wuce Villa da ita, zo kaga murna Hajiya ta warke kowa sai farinciki yake duk sun haɗu harda su Fatuu, a can Katsina ma sai murnar jin Hajiya ta samu lafiya ake, anan Villa aka cigaba da kula da ita tana shan magunguna, bayan tayi sati biyu ya kama watan ta guda a Abuja lokacin ta warke sosae har ɗan ƙara jiki tayi da haske tace ma President tana son komawa Katsina nan fa ya shiga roƙonta kan ta haƙura da zaman Katsina taci gaba da zama nan amman ta nuna mashi ita tafi son zaman can, koda Hajiya Maryam taji itama zuwa tayi suka haɗu da President ɗin suna roƙonta kan ta zauna nan Hajiya Maryam harda yin ƙwalla tana faɗin su basu son su rasata ne yanzu da basu yi gaggawar ɗaukkota nan ba da Allah kaɗai yasan mi zai faru Hajiyar na murmushi tace abunda Allah ya ƙadarro shi zai faru da lokacinta yayi sai ta tafi kuma a tunaninta su suka sa ta warke ne, Hajiya Maryam ɗin tace eh duk da hakan dai gara ta zauna anan tafi samun kulawa, ƙarshe dai saida suka yi nasarar tursasa mata ta dawo nan amman tace masu dole zata koma tayo sallama da mutane Hajiya Maryam harda cewa in don wannan ne ai sai suje rana ɗaya tayo su dawo tace a'a tana buƙatar lokaci ba wai daga taje zata dawo ba don haka aƙalla zata yi wata guda Hajiya Maryam tasa rigimar gaskiya yayi yawa da ƙyar aka tsaya kan sati biyu shima saida Hajiyar ta kafe kafin ta amince, kafin su tafi ne tace tana son bar masu wasiyya ko ba yanzu ba in ajali ya risketa tana son kada su tada Tk daga gidanta koda zasu yi amfani da gidan to a ware mashi isasshshen wurin da zai zauna ta bashi halak malak sannan su Saude ma a barsu suci gaba da zama har sai in su suka buƙaci tashi ko kuma su in suna buƙatar su tashi to sai su siya ma Sauden gida, gaba ɗaya suka haɗa baki wurin cewa in sha Allahu zasu yi kamar yadda tace Hajiya Maryam tace amman ta daina faɗin wasiyyar nan tana tada masu hankali, Hajiyar tayi yar dariya tace to miye abun tashin hankali abunda ya zama dole da lokacinta yayi kuma su ai yan gata ne tunda sun rayu da ita tsawon lokaci wasu da yawa ma basu san Mahaifiyarsu ba, Hajiya Maryam ɗin tace duk da hakan dai suna roƙon Allah ya yasa su cigaba da rayuwa da ita tsawon lokaci tana murmushi ta amsa da Amin, bayan kwana biyu ta dawo Katsina harda First Lady da Aunty suka rakota, zo kaga murna Hajiyar Sanata ta dawo kar ma su Tk gaba ɗaya bakunansu sun ƙi rufuwa dama Tk kusan yafi kowa shiga damuwar ciwon nata zuciyarshi tay ta raya mashi kodai mutuwa Hajiyar zata yi shi bama damuwar shi makomarshi ba a'a yadda zai rayu babu ita shine yafi tada mashi hankali don ba ƙaramin shaƙuwa yayi da ita ba ko Mahaifiyar shi bai jinta a ranshi kamar yadda yake jin Hajiya, Mutane sai so suke su shigo gidan suga Hajiya amman ba dama don ƙopar gidan dankam take da Security wasu kuma sun zagaye gidan wanda babu wasa a tattare dasu gasu da manyan makamai, su Gwaggo dai sun shiga har sun gaisa da Mom da Aunty sun masu ya maijiki, haka manyan mutane mata da maza da yan siyasa sun zo duk an barsu sun shiga sun gaisa da su Mom tare da yi masu ya mai jiki har Governor da First Lady ɗin Katsina sun zo unguwa fa ta ɗinke ba abunda kake gani sai motoci masu numfashi da jiniya, Washe gari su Mom suka tafi bayan tafiyarsu ne Tk ya faɗi ma Hajiyar mutane yan unguwa nata son su shigo su gaishe ta an hana su, tana jin hakan ta bada iznin duk wanda yazo a barshi ya shigo nan fa yan unguwa sukai ta shigowa dubiya manya da yara da dattawa Hajiya tayi amfani da wannan damar duk wanda yazo gaidata sai tayi mashi bankwana ta nemi yafiya, gaba ɗaya gwuiwar mutane sai tayi sanyi kuma jin Hajiyar zata bar Katsina harda masu yin ƙwalla tun ma ranar tafiyar bata yi ba, kowa ya nuna rashin jin daɗin tafiyar da zata yi tana ta ce masu kada su damu ai ba shikenan an rabu ba indai da sauran rayuwa za'a cigaba da zumunci kuma ga Tukur nan zai cigaba da zama a gidan don haka ba abunda zai fasu tsakaninsu, tunda su Tk da Saude da Husnah suka ji zancen komawar Hajiyar Abuja gaba ɗaya suka shiga damuwa kowa jikin shi yay sanyi, bayan dawowarta da sati ɗaya ne ranar Friday da daddare ta kira Tukur da Saude a cikin Bedroom ɗinta, a kan carpet suka zauna ita kuma tana zaune a bakin gado idanunta sanye a cikin gilashi, sun ɗan ɗauki lokaci shiru tana ta kallonsu su kuma duk sun sunnar da kai yayin da ƙirjinsu ke bugawa tamkar ana masu luguden ta6are can Hajiyar ta nisa kafin a nutse ta fara magana,
"Na buƙaci ganin ku ne don yin maganar da nasan bazaku ta6a jin daɗin ta ba kamar yadda nima ba don daɗin yasa zanyi maku ita ba, da farko dai ina mai matuƙar godiya a gare ku godiya mara iyaka, gaba ɗayan mu bamu da wata dangantaka ta jini face ta kasancewar mu musulmai amman Allah ya haɗamu muka zauna tare tsawon lokaci har muka zama tamkar dangin juna, ina son ku sani, ku mutane ne masu matuƙar muhimmanci a gare ni wanda wasu ma da yawa da nike da alaƙa ta jini dasu basu da irin muhimmancin a wurina, Tukur, kai tamkar ɗan dana haifa kake a wurina duk da kafi kama da jikana amman kallon ɗana na jini nake maka, haka kema Saudatu ina matuƙar jin ki a rai na ba kuma don hidimar da kike man ba sai don ƙaunar ki a gare ni wadda nasan ita tasa kika zauna tsawon lokaci kina hidimta man ba tare da gajiyawa ba kuma daidai da rana ɗaya bazan iya cewa ga lokacin da kika sa6a man ta hanyar yi man rashin biyayya ko makamancin hakan......to, gaba ɗaya dai ba abunda zance sai dai ince maku Nagode, Nagode Allah ubangiji ya saka maku da mafificin Alkhairinsa ya ji6anci al'amuranku, ina kuma roƙon shi da yadda ya haɗa mu a gidan duniyar nan ya haɗa mu a gidan aljanna muci gaba da yin rayuwa tare, nasan bazaku rasa jin zancen komawata Abuja ba duk da bamuyi maganar da ku ba kafin yanzu, nasan dole kuji ba daɗi amman ina mai baku haƙuri dama haka rayuwa ta gada in har aka haɗu to tabbas wata rana sai an rabu koda kuwa ba mutuwa ba, don haka inason ku kwantar da hankalinku dan na tafi ba yana nufin an rabu ba kenan indai da rayuwa dole aci gaba da zumunci, kai Tukur zaka cigaba da zama a gidan nan koda kuwa bayan bani a duniya kana da kaso a cikin sa so nike Hajiyar Sanata taci gaba da wanzuwa ta dalilin ka, haka kema Saudatu zaku cigaba da zama keda mijinki har zuwa lokacin da kuke so ke bazance ki zauna dundundun ba saboda yanayin aikin mijinki a koda yaushe za'a iya canza mashi wuri dama ni na roƙa aka bar man shi tsawon lokaci muna tare ba'a ɗauke shi ba saboda ina jin daɗin zaman shi sai kuma yazo ya aure ki aka ƙara zama ɗaya...., akwae gida da nike son siya maki koda bani ba na faɗa za'a siya maki in kun buƙaci barin nan, A ƙarshe ina mai ƙara godiya a gareku sannan ina roƙon yafiyarku saboda ance zo mu zauna zo mu sa6a indai nayi maku ba daidai ba da sani na ko akasin hakan ina mai roƙon ku da ku yafe man ni dai na yafe ma kowa sannan ina mai roƙon ku da kuci gaba da kyautata ma abokan zaman ku",
Saida ta gama Magana ta fahimci gaba ɗaya kuka suke jin sheshshekarsu tay shiru tana kallon su dama itama ƙarfin hali kawai take, bayan wani lokaci tace "To duk kun tasani a gaba kunata kuka ko nima so kuke ɗan ƙarfin halin da nike in karaya in sa kukan ne?" a tare suka haɗa baki cikin muryar kuka suka ce "a'a......" tace to su daina suyi haƙuri don Allah tun farko tasan dama dole suji ba daɗi to amman sai ayi haƙuri wataƙil dama Allah ya ƙaddaro zamanta Abujan ne tunda tuntuni suke son ta koma taƙi hardai yanzu sukai galabar sata ta koma suyi haƙuri ai ba'a rabu ba kenan kamata yay ma su gode ma Allah daya sa ta miƙe, nasiha sosae tayi masu suna ta sharar ƙwalla daga ƙarshe tace suje, har zasu miƙe tace to su basu yafe matan ba wannan magana ba ƙaramin ta6a masu zuciya tayi ba duk suka ce mata su wllh ba abunda ta ta6a yi masu ba daidai ba tace duk da haka dai su yafe mata, a tare suka haɗa baki suka ce sun yafe mata tare da yi mata Addu'o'i, bin su tayi da ido lokacin da suka nufi ƙopa, bayan fitar su ta maido idonta tana kallon gabanta can ta sa hannu ta ɗaga gilashin idanunta ta goge ƙwallan da suka gangaro mata...........
104
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
.........Suna fitowa Tk ya wuce ɗakin su Saude kuma ta nufi baya inda ɗakinta yake, a bakin gado ya zauna yaci gaba da yin kukan mai cin rai yana haka Husnah ta shigo ciki ma gareta har ya girma, zama tayi a kusa dashi fuskarta ɗauke da damuwa ta shiga bashi haƙuri kai kawai yake ɗaga mata, da yake tasan wurin Hajiya suka je cike da damuwa ta tambayeshi tafiyar dai zata yi da gaske ya ɗaga mata kai alamar eh ta ɗan girgiza kai itama duk wani iri take ji can ta kai hannu ta fara goge mashi ƙwallan tana bashi haƙuri, Saude ma tana komawa ɗakinta ta faɗa gado ta saka kuka mai sauti gwanin ban tausayi, ta ɗan ɗauki lokaci kafin Officer ya shigo ya isketa a haka, da alamun tashin hankali ya nufi bakin gadon ya zauna ya kai hannu yana ta6ata tare da kiran sunanta yana tambayarta lafiya miya faru, cikin kuka tace mashi da