Showing 453001 words to 456000 words out of 512766 words

Chapter 152 - Asanadin Makwabtaka Book 3 Hausa Novel Complete

Unknown   

27 Dec 2024

1534

sukai sallama. Da yamma bayan sallar la'asar sai ga Baban su Umar yazo shagon Amadu cikin fara'a suka gaisa kafin cike da farinciki yake sanar dashi ɗazun mijin yar'uwar shi ya kira shi yake ce mashi yana buƙatar siyan gidan da yake ciki ne shine yace zai siya mashi gida da zai zauna har ma yace mashi ya nemi gidan da yake so in ya samu sai yayi mashi magana, sam Amadu bai kawo komai a
ranshi ba ya nuna ya taya shi murna sosae, Bayan sallar isha Tk ya samu Hajiya a parlonta daga gefenta ya zauna ya gaishe da ita tana murmushi ta amsa, shiru yay ya maida kan shi ƙasa yana wasa da yatsun hannunshi Hajiya ta lura da Magana yake son yi tace "Ya akai ɗan gidan Hajiyar Sanata mi ake son faɗi man ne?" ɗagowa yay yana murmushi ya kasa mata magana tace mashi ko sun fara yar kunya ne still murmushin yake bai ce mata komai ba tace kar yaji komai ya fadi mata abunda yake son fadi mata da ƙyar yana yar in ina yace dama so yake a je a nemo mashi Aure, ɗan buɗa ido tay tana kallonshi tace "Wato ashe dama kana da wadda kake so shine tuntuni kaƙi yin niyya sai yanzu da kaji abokin ka zaiyi kana gudun yayi ya barka ko" yana ɗan sosa kai yace a'a yaga bai fara aiki ba shiyasa bai yi niyya ba tace to yanzu aikin ya fara ne yay shiru yana murmushi,

"Ai ganin baka da niyya yasa banyi Maganar a nema maka aikin ba tunda mi zakai da aiki ba iyali amman yanzu tunda kayi niyya zanyi magana sai a nema maka sai kayi Addu'a Allah yasa a dace, Maganar zuwa nema maka aure kuma zan yi ma mahaifinka magana amman tukunna sai ansan wacece kake so tunda ba'a kama nema maka aure ba tare da anyi bincike ba" dakatawa tayi kafin ta tambaye shi sunan yarinyar da kuma yar gidan waye ya faɗi mata sunanta Asma'u tare suka yi karatu har ya kwantanta mata ita yace sun ta6a zuwa ta gaishe da ita Hajiyar tace ta ganeta yanzu zata sa ai bincike sosae kafin tayi ma Mahaifin nashi magana sai a turo mutum ɗaya ko biyu itama zata kira Kawu Mani sai su haɗu suje, Godiya yayi mata tare da Addu'o'i tana murmushi tace Allah ya nuna mata bikin Tukur ɗan autanta yana murmushi ƙasa ƙasa yace Amin kafin yayi mata sallama ya tafi.

Washe gari bayan sallar La'asar sai ga Abbas yazo tare da wasu Mutane bayan sun gaisa da Amadu ya tambayeshi Gwaggo na nan ne yace mashi eh, juyawa yay wurin Motar mutanen da suka zo tare su biyu yace masu yana zuwa suka furta Ok ya juyo ya nufi gidan, a bakin ƙopar zauren ciki ya tsaya yana sallama Gwaggo ta leƙo daga cikin falo tana amsawa tana ganin shine ta washe baki tana faɗin "ɗana Abbas ashe kai ne ka shigo mana" yana murmushi ya nufo falon Gwaggon ta koma ciki, bayan ya shiga a kujera ya zauna suka gaisa ta tambayi su Abdul yace mata duk suna lafiya kafin yace mata yaji abun murna na auren Amadu Allah ya sanya alkhairi tana fara'a ta amsa da Amin, ce mata yay dama yazo tare da injiniyoyi zasu duba gidan da alamun rashin fahimta Gwaggon tace gida kuma ganin yadda tayi Maganar yasa yace mata basu yi Magana da Haisam bane akan aikin da za'ayi a gidan da sauri ta girgiza kai tace gaskiya basu yi Magana ba sai dai ko Amadu, yar dariya Abbas yayi yace ina ruwan H,Zakee nan ya shiga yi mata bayanin aiki za'a ma gidan don har ma anyi cinikin gidan dake makwabtaka dasu Haisam ɗin ya siya za'a haɗe da wannan ayi sabon gini, zaro ido Gwaggo tayi baki buɗe take kallon shi a ɗan ruɗe tace "anya dai ɗana Abbas haka maganar nan take" yana dariya yace mata tabbas haka take ƙilan da Amadu sukai maganar, cike da mamaki tace anya ai daya faɗi mata amman bari ta kira shi taji, wayarta ta ɗaukko ta shiga kiran nashi bayan ya ɗaga tace mashi ya shigo yanzun tana son ganinshi, bada daɗewa ba ya shigo da sallama ya nufi kujera ya zauna yace mata gashi, tambayar shi tayi ko sunyi maganar za'ayi aikin gidanan da ɗanta Haisam da alamun rashin fahimta ya girgiza mata kai alamar a'a kafin ya faɗi mata yadda sukai dashi game da gidansu Umar da lambobin daya tura mashi sai kuma zuwan da Babansu Umar yayi cike da farinciki ya bayyana mashi sunyi waya da shi yace yana buƙatar siyan gidan da yake ciki shi kuma zai siya mashi wani ya zauna, Abbas na murmushi yace to ai su ya siya ma gidan za'a haɗe da wannan a maida shi babban gini shi ya ɗaura ma kan aikin shine ma yazo da injiniyoyi don su fara duba gidajen, gaba ɗaya Gwaggo da Amadu idanunsu a waje suke kawu Amadu ya kai hannu ya rufe baki alamar Al'ajabi da alama mamaki ya kashe masu bakuna can da tsananin mamaki kawu Amadu yace "Wai Yaya Abbas yanzu kana nufin saboda mu ya siya gidan su Umar ɗin kuma har ya siya masu suma gida?" kai Abbas ya ɗaga mashi yace eh a yadda sukai za'a haɗe sai ai babban Flat a fidda ma Gwaggo part ɗinta sai shima Amadun a fidda mashi nashi da zai zauna da iyalinshi harda ma 6angaren baƙi, nannauyar ajiyar zuciya Gwaggo ta sauke ta shiga girgiza kai da alamun damuwa tace "Amman gaskiya ɗana Abbas wannan hidiman tayi yawa sosae ace ya siya masu gida sannan ya siya wanda suke ciki kuma a haɗe da wannan a fara sabon gini yadda gini kede cin kuɗi ai gaskiya abun yayi yawa nidai da za'a bi ta tawa don Allah ya barshi in ma dole so yake yayi to a gyara wannan namun kawai ni sai in koma can ɗayan ɗakin shi kuma Amadun sai su ɗauki dakina da nan falon za'a ma iya ƙara girman falon tunda ga ɗan sauran wuri nan daga gefe har banɗaki ma za'a iya yi masu a ƙuryar lafiya lau wannan ma zai ishe mu" fuskarta ɗauke da damuwa tayi maganar Abbas na dariya yace "to Gwaggon mu waya ƙi cigaba tunda shi yayi niyya yana da halin yi ne karki wani damu tunda daya san zai takura da bazai fara cewa zai yi ba, a yadda ma ya faɗi man dama yana ta son a canza ginin gidan to yadda yake son a maida gidan bazai isa ba kuma yasan kun riga kun saba da unguwar bazaku ji daɗi ba in ya yi maku ginin wani wuri Hajiya ma yasan bazata so ku rabu ba shine yanzu yay tunanin yin hakan harma anyi cinikin gidan ya biya shi kuma wanda aka siya ma gidan dama can yanada rabo a wurin shi ne, yanzu dai na bar mutane a waje zan iya masu magana su shigo?" duk tayi sukuku da ita ta ɗaga mashi kai alamar eh ya miƙe yana dariya yana faɗin karta wani damu abun farinciki ne don haka tayi farinciki kawai ta ɗan yi murmushi ya juya kan Amadu da yayi duruduru yace ya taso yaje gidan su Umar ɗin yaga in mai gidan na nan yace za'a shigo a duba yace to tare da miƙewa suka fita, Gwaggo dai tayi zuru tana ta jinjina abun a ranta tasan dole gidan su Umar ɗin yayi kuɗi don yafi nasu girma ga gida kuma da aka siyan masu sannan azo a dasa gini, Bayan duk sun gama dubawa Abbas yace ma Gwaggo za'a kawo hotunan gidaje sai su za6a tace to kawai sukai sallama, zaune sukai falon Gwaggo ta kasa yin magana sai Amadu dake ta faman jinjina abun yana faɗin to wai hakanan ya yanke yi masu ginin ko kuwa dai yaji batun gyaran gidan saboda aurenshi shine zai yi masu, wannan Maganar da yayi yasa Gwaggo ta ɗaukko wayarta ta shiga kiran Fatuu, bayan ta yanke Fatun ta kira suka gaisa nan take tambayar ta wai sunyi maganar gyaran gida da tace mata tana son ayi kafin bikin Amadu da Haisam ne tace mata a'a kawae dai ta sanar mashi zancen shine ya tambayi yaushe za'a saka rana ta fadi mashi yadda sukai da ita na ba yanzu ba sai an yi gyaran gidan Gwaggon ta sauke ajiyar zuciya, da sauri ta tambayeta miya faru ne nan ta kwashe komai ta faɗi mata ita kanta Fatun tayi mamaki sosae ido waje ta shiga jinjina Maganar aikin tace gaskiya hidiman tayi yawa sosae Gwaggon tace wllh itama duk ta damu Fatun tace bari tayi mashi magana gaskiya in ma aikin yake son yi masu to a gyara gidan nasu kawai Gwaggo tace itama abunda tace kenan to Abbas yace ai har ya riga ya siya gidan kuma shi Baban su Umar yanzu in aka hana yana iya ganin anyi mashi baƙin ciki, tana cikin yin Maganar Amadu ya miƙa hannu ta bashi wayar bayan sun gaisa da Fatun yace mata kawai a kyaleshi ai mashi godiya yanzu ko anyi mashi magana kan ya bari sun san dai ba fasawa zai yi ba, a sanyaye tace shikenan sukai sallama,

Bayan sun gama yin wayar Haisam ta shiga kira da yake su safiya ce yana wurin aiki, bayan yayi picking tace mashi tana son suyi vedio call ya furta Ok, yana zaune a Office ɗin shi jikinshi sanye da baƙaƙen suit fuskar shi sai annuri take, fuska a tur6une ta gaishe dashi yana ɗan murmushi ya amsa ya gane laifi yayi mata daga yanayin face ɗinta, daga gaisuwar tayi shiru tana ta tura baki, lumshe mata ido yay ya furta "ya akai ne My Baby?" wani kallo tayi mashi a marairaice tace taji abunda yayi amman gaskiya hidiman yayi yawa in aikin za'ayi to ayi iya gidansu basai ya kashe uban kuɗi ba haka, murmushi kawai yake ganin har yanzu halinta na rashin son ya kashe kuɗi sosae na nan, ganin bai ce komai ba ta tura baki tace bazai yi magana ba,

"Yanzu nayi laifi don zan ma Family ena abu?" ya tambaya tare da ɗage mata gira, kaman zatayi kuka tace "a'a ni bance kayi laifi ba Amman gaskiya kashe kuɗin zai yi yawa" sigh yay still murmushi yake yace "bazai yi yawa ba akwae kuɗin Baby so don't worry" yamutsa fuska tayi tace to in suka ƙare fa har saida yayi yar dariya ganin taƙi ta girma har yanzu tana behaving kamar da yarintarta duk da yasan yanzun ma ba wani girma tayi ba tunda yanzu take 20yrs, yana yar dariya yace mata bazasu ƙare ba saboda yana dasu da yawa akwae Dollars ya tara cike da tsokana yayi Maganar ta zaro ido ya ɗage mata gira,

murmushi tay tace "baka tsoron insa ai kidnapping ɗinka kana faɗi man ka tara Dollars" dariya yay har haƙoranshi suka bayyana yace ai tuntuni ta riga tayi kidnapping ɗin Heart ɗinshi yanzu ko duka kuɗin dake gareshi tace ya bata zai tattara ya bata, wani kallo tayi mashi tace is he serious ya jinjina mata kai yace amman zai fidda na aikin gidan da za'ai don kar aga yayi magana biyu sai kuma wanda zai ciyar dasu kafin ya sake tara wasu kada Allah ya kama shi ya barsu da yunwa, wani irin kallon ƙauna ta shiga bin shi da shi shima kallon nata yake idanu a ɗan lumshe cikin sanyin murya ta furta mashi "Thank you for loving me unconditionally Hubby. You have shown me what true love is, and I am forever grateful for that. I couldn't imagine my life without you" tana gama Maganar kwalla suka zubo mata sharrr, lumshe ido yay tare da ɗan murmushi yasa yatsa saman screen ɗin yana yin alamar goge mata ƙwallan hakan yasa ta yi yar dariya, Godiya ta shiga yi mashi sosae da Addu'o'i a hankali yake amsa mata daga baya sukai sallama cike da nuna ƙauna, a ranar haɗaɗɗun abinciccika suka haɗa mashi ita da mai aikin su da daddare kuwa duk da halin da take ciki saida ta tabbatar tayi mashi godiya ta hanyar gigitashi ta yadda har saida suka zubda hawaye su duka..........

101

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~



.......Ranar Alhamis Hajiya ta kira kawu Mani na Daura ta tambaye shi gobe Juma'a zai shigo Katsina ne yace mata a'a amman in tanason ganin shi sai yazo tace mashi in bazata takura shi ba tana son ganin shi yace to ba damuwa zai shigo.

Washe gari kafin ayi salla ya iso Ya yi shigar manyan kaya ya fito a dattijo mai kamala anan gidan yayi sallar Juma'a suka ci Abinci tare da Hajiya a dining, bayan sun gama cin abincin ne suka dawo falo yana zaune a kujerar dake gefen ta Hajiya yace "Hajjaju gani na amsa kira Allah yasa na lafiya ne" tana murmushi ta bashi amsa da lafiya lou sai alkhairi ya furta Alhamdulillah shi suke fata a koda yaushe, Maganar zuwa neman auren Tk tayi mashi tace tana son ya shige gaba tasa anyi mata bincike akan gidansu yarinyar an tabbatar mata da basu da matsala shi mahaifin nata asali mutumin Gombe ne aikin custom ya kawo shi Katsina daga nan zaman ya ɗore don yanzu har ma yayi retired to tana son ya tuntube shi kan su bada lokacin da za'aje neman auren, jinjina kai yayi yace to ba matsala a yau ma kafin ya tafi sai ya tuntube shin a bashi Address ko kuma lambar wayar shi tace to dama ta amshi lambar a wurin tukur ɗin, bashi lambar Baban Asma'un tayi yayi saving ya ɗago yana murmushi yace ashe sun kusa shan bikin ɗan gidan Hajiya itama murmushin take tace aikuwa yay fatan Allah ya sanya alkhairi ya nuna masu,

bayan ta amsa da Amin tace "Kai ma in kana son ƙara Auren akwae mata a ƙasa zan baka" waro ido yay ya ɗan buɗa baki sai kuma yayi dariya yace yasan ai wasa take, ɗan ta6e baki tayi tace dama ana wasa da Maganar aure, yana dariya ya tambayeta wacece matar, tace "Kana so ne?"

"To Hajjaju taya zansan ko ina so ba tare dana ganta ba" yana ta dariya yay Maganar,

"To ai in kai baka santa ba ni na santa kuma na yaba da ita ne shiyasa nayi maka maganarta tuntuni ma nake kwaɗayin wani cikin Family ya aureta saboda kyawun halinta Allah bai nufa nayi ma wani maganarta ba sai kai da nayi mawa yanzu",

"To ai Hajjaju kyau dai in ganta" still dariyar yake itama haka tace "ai ina ganin ma kasan wacece Kakar matan su Haisam da Nameer ce, ba wani tsufa tayi ba kawai don anyi mata auren wuri ne da yake asalin Fulanin daji ce in ba don haka ba bazata aje ma jikoki kamar su ba don ina ganin ka girmeta kaga kai baka dade daka samu Yan jikokin ba" shiru yay yana ƙoƙarin tuna ko yasanta can yace gaskiya ya kasa ganeta koda ya santa Hajiyar tace bari taga ai kaman akwai hotonta da akayi da bikin su Nameer anan falonta kuma shima ranar yana nan dashi akai hotunan, hoton gwaggo da tayi tare da Mino a ranar ta buɗo mashi ta miƙa mashi ya amsa ya bi hoton da kallo yana ɗan murmushi can ya ɗago ya tambayi Hajiyar bata da aure ne tace inda tana dashi zatayi mashi tayin auren nata ne ya sake tambayar abunda ya rabata da mijin nata ta faɗi mashi aurenta biyu na farko na dole ne akai mata da yake ta taso marainiya shine kawunta da ya riƙeta ya aura mata abokin shi to hardai zaman ya ƙare basu haihu ba bayan ta dawo wurin kawun nata Daura tana zuwa tallan nono a kasuwar mashi Allah ya haɗa ta da mijinta na biyu data aura shine suka haifi yara biyu kafin ya rasu sanadiyyar haɗarin mota tun daga nan kuma bata ƙara yin aure ba kusan shekara ashirin da biyar duk da tana da masu son auren nata itace bata so cikin dangin mijinta daya rasu wani ya samo mata aikin asibiti tana yi farko ma a gidan shi ta fara zama daga baya saboda rashin jituwar da suke samu da matarshi ta baro mashi gidan tazo ta gina wannan da take ciki a filin da suka gada, nan ta bashi labarin yadda mahaifiyar Fatuu tayi aure ta haifesu su biyu da yadda Gwaggon ta ɗaukko su ta riƙe ta kuma shiga nuna mashi kyawawan halayenta, ajiyar zuciya Kawu Mani ya sauke ya sake kallon hoton gwaggon kafin ya miƙa ma Hajiya wayar ta amsa tare da tambayar tayi mashi ko kuwa yana yar dariya yace tunda tayi mata tana son ya aureta in dai zata amince zai auretan,

"A'a ba wani tunda tayi man inason ka aureta salon kaja man matanka su ƙullace ni, kawai in kaji kana son ta zaka aureta to in kuma bata yi maka ba lafiya lau ka fito ka faɗi man ai ba wani abu bane dama don naga kana da ra'ayin mata fiye da ɗaya ne tunda yanzu haka biyu gareka shiyasa nayi maka Maganarta" sosae yake dariya jin abunda tace bayan ya tsagaita yace to yanzu koda tayi mashin in ita taƙi amincewa dashi fa tunda tace tana da masu son aurenta itace bata so Hajiyar tace ai sai suma su jaraba sa'ar su ƙilan Allah yasa ta amince dashi, gyaɗa kai yay yace to yanzu ya za'ai tasan dashi,

"Wannan mai sauƙi ne in ka shirya haɗuwa da ita kuyi magana sai in kirata in mata magana", yar ajiyar zuciya ya sauke yana murmushi yace abunda za'ai yanzu zai kira mahaifin ita wadda tukur ke so yayi mashi maganar haɗuwarsu in ya bashi dama da yayi sallar la'asar sai ya tafi yanzu abunda za'ai tayi ma ita Matar magana in ya fita sai ya fara tsayawa wurinta su gaisa

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login